Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya Afrika
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91 Afrika
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu Afrika
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika

Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO
Published: December 15, 2025 at 8:55 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu kwararru kan harkokin tsaro a Amurka sun ce tayin da kasar Ukraine ta yi na yin watsi da burin neman shiga cikin kungiyar kawancen tsaro ta NATO, bai kai wanda zai iya canja akalar tattaunawar neman sulhun da ake yi yanzu ba.

A lokacin tattaunawa da wakilan Amurka ranar lahadi a kan shirin sulhu tsakanin Rasha da Ukraine, shugaba Volodymyr Zeklensky yayi tayin watsar da yunkurin da kasarsa ke yi na neman shiga kungiyar kawancen tsaro ta NATO.

Shugaban yace maimakon neman shiga NATO, kasar zata nemi tabbacin na tsaro, watau kariya daga Amurka da kasashen Turai da wasunsu.

Daraktan nazarin tsaro da manufofin hulda da kasashen waje cibiyar nan ta CATO institute, Justin Logan, yace wannan tayin ba zai canja komai a tattaunawar neman sulhun da ake yi ba, yana mai fadin cewa wannan wani yunkuri ne kawai da Ukraine keyi na neman nuna cewa tana son a yi sulhu.

Logan da wani farfesa na nazarin muhimman muradu na kasa a Jami’ar Florida, Andrew Michta, sun ce da ma zai yi wuya ga Ukraine ta samu shiga kungiyar ta NATO, saboda haka wannan ba wani muhimmin batu ba ne a yanzu.

Sai dai kuma, ba kowa ne yayi watsi da tayin na Zelensky ba amma wani tsohon mai bada shawara kan hulda da kasashen waje a gwamnatin shugaba Obama , Brett Bruen, yace wannan sassauci da Ukraine ta yi babba ne kuma yana da muhimmanci, domin kuwa Zelensky yana nuna ma duniya cewa shi mai neman zaman lafiya ne، yayin da har yanzu babu wani abu guda da kasar Rasha ta nuna sassauci a kai daga cikin bukatunta.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa
Next Post: Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika
An Bukaci Sabbin Shugabanni Su Yi Jagoranci Nagari da Inganta Ayyukan Jama’a Labarai
Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
Iran Tayi Allah Wadai Da Kai Hari Cibiyar Pars Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika
Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika
  • Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Man Fetur A Najeriya Afrika
  • Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis Afrika
  • Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka
  • ‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.