Jihar Gombe a Arewa Maso Gabashin Najeriya ta yi alfahari tare da maraba da ’yarta, Maryam Ibrahim Dan’azumi, wadda ta zama zakarar gasar Alƙur’ani ta ƙasa da ƙasa ta Sarki Abdulaziz karo na 46 da aka gudanar a Makkah Kasar Saudi Arabia.
Maryam ta wakilci Najeriya a rukunin haddar Alƙur’ani gaba ɗaya, karatu, Tajweed da Tafsiri, inda ta yi galaba a kan mahalarta daga ƙasashe daban-daban, ta zama gwarzuwar gasar ta duniya, tare da ɗaukaka martabar Gombe da Najeriya.
Wannan nasara ta ƙara zama abin tarihi, domin gasar ta bana ita ce karo na farko a cikin shekaru 46 da aka fara bai wa mata damar shiga gasar.
Daga nasarar da ta samu a matakin Ƙaramar Hukumar Gombe, zuwa matakin jiha, sannan ta zama gwarzuwar Najeriya, Maryam ta nuna ƙwazo, jajircewa da ƙwarewa wajen haddar da karatun Alƙur’ani Mai Girma.
Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya Maryam, iyayenta, malamanta da daukacin al’ummar Musulmi murnar wannan gagarumar nasara, yana mai bayyana ta a matsayin abin alfahari da kuma abin ƙarfafa gwiwa, musamman ga ’yan mata.


