Shugaba Felix Tshisekedi na kasar Kwango ta Kinshasa, ya zargi Rwanda da laifin karya alkawarin da ta dauka karkashin yarjejeniyar zaman lafiyar da Amurka ta kulla tsakaninsu, da nufin kawo karshen yakin shekara da shekaru a gabashin wannan kasa mai dimbin arzikin ma’adinai.
Shugaba Tshisekedi yayi wannan zargi a jawabin da yayi gaban ‘yan majalisar dokoki, kwanaki kadan a bayan da ya halarci taron rattaba hannu kan yarjejeniyar a Washington.
Ya zuwa yanzu dai, babu wani martani da aka ji kan wannan zargi daga kasar Rwanda.
Wani jami’in Amurka yace gwamnatin shugaba Trump tana nazari da sa ido kan halin da ake ciki, tare da aiki da dukkan kasashen, kuma tana sa ran za a dauki matakan gaggawa na aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar.
Kazamin fadan da ake yi yana kawo tsaiko ga fara aiwatar da yarjejeniyar, wadda Amurka da Qatar suka kulla tsakanin Kwango da Rwanda da kuma kungiyar ‘yan tawayen M23. A karshen makon nan, mayakan kungiyar M23 sun kutsa kusa da bakin iyaka da Burundi, inda suka kama wani gari mai suna Luvungi.
Rwanda ta musanta zargin cewa ita ce uwargidan ‘yan tawayen na M23.


