Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Rwanda Tana Keta Yarjejeniyar Zaman Lafiya – Tshisekedi
Published: December 9, 2025 at 3:28 AM | By: Ibrahim Alfah Ahmad

Shugaba Felix Tshisekedi na kasar Kwango ta Kinshasa, ya zargi Rwanda da laifin karya alkawarin da ta dauka karkashin yarjejeniyar zaman lafiyar da Amurka ta kulla tsakaninsu, da nufin kawo karshen yakin shekara da shekaru a gabashin wannan kasa mai dimbin arzikin ma’adinai.

Shugaba Tshisekedi yayi wannan zargi a jawabin da yayi gaban ‘yan majalisar dokoki, kwanaki kadan a bayan da ya halarci taron rattaba hannu kan yarjejeniyar a Washington.

Ya zuwa yanzu dai, babu wani martani da aka ji kan wannan zargi daga kasar Rwanda.

Wani jami’in Amurka yace gwamnatin shugaba Trump tana nazari da sa ido kan halin da ake ciki, tare da aiki da dukkan kasashen, kuma tana sa ran za a dauki matakan gaggawa na aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar.

Kazamin fadan da ake yi yana kawo tsaiko ga fara aiwatar da yarjejeniyar, wadda Amurka da Qatar suka kulla tsakanin Kwango da Rwanda da kuma kungiyar ‘yan tawayen M23. A karshen makon nan, mayakan kungiyar M23 sun kutsa kusa da bakin iyaka da Burundi, inda suka kama wani gari mai suna Luvungi.

Rwanda ta musanta zargin cewa ita ce uwargidan ‘yan tawayen na M23.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne
Next Post: Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar Amurka
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Man Fetur A Najeriya Afrika
Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika
Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya Sauran Duniya
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
  • Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.