Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
Published: February 10, 2026 at 7:43 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 11, 2026

Uwargidan Gwamnan jihar Gombe, Hajiya Dakta Asma’u Inuwa Yahaya,ta jagoranci wani muhimmin taron wayar da kai da nufin ƙarfafa matakan dakilewa da kuma sauya ɗabi’un zamantakewa domin kawo ƙarshen cin zarafin mata da ‘yan mata.

An gudanar da taron ne a Cibiyar Ilimi wato (Education Resource Centre) da ke Tashan Dukku a birnin Gombe, tare da halartar jami’an gwamnati, shugabannin al’umma da na addini, ƙungiyoyin fararen hula, ƙungiyoyin mata, da kuma abokan hulɗar ci gaba.

Shirin, wanda aka aiwatar tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Matan Gwamnonin Nijeriya da kuma tallafin gidauniyar Ford Foundation, ya gudana ne ƙarƙashin taken: “Wayar da Kai don Rigakafi: Sauya Ka’idojin Zamantakewa da Ƙarfafa Ƙudurin Jiha Don Kawar da Cin Zarafin Mata.”

A jawabinta, Hajiya Dakta Asma’u Inuwa Yahaya Wacce Kwamishinar Ma’aikatar harkokin Mata Asma’u Mohammed Iganus ta wakilta ta jaddada cewa rigakafi shi ne hanya mafi tasiri wajen magance matsalar cin zarafi sannan ta bayyana cewa sauya tunani da halayen da ke goyon bayan danniya da take hakkin mata na da muhimmanci wajen gina al’umma mai adalci da mutunta juna.

Uwargidan Gwamnan ta kuma tabbatar da ƙudurin gwamnatin Jihar Gombe na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su kare haƙƙin mata da ‘yan mata, tare da samar da ingantattun hanyoyin kai ƙorafi da tallafa wa waɗanda abin ya shafa.

Masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yi kira ga haɗin kai tsakanin gwamnati, al’umma da ƙungiyoyin fararen hula domin tabbatar da cewa an kawo ƙarshen cin zarafin mata a kowane mataki. Sun kuma yabawa gwamnatin jihar bisa matakan da take ɗauka wajen ƙarfafa tsarin kariya da inganta walwalar mata da yara.

Taron ya kasance wani muhimmin mataki na ƙara wayar da kai da kuma gina aniyar haɗin gwiwa domin samar da al’umma mai zaman lafiya, adalci da mutunta haƙƙin bil’adama.

Ga Rahoton Aliyu Gerengi Gombe Daga Gombe

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/GBV-GOMBE.mp3
Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
Next Post: Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka Amurka
  • Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
  • Amurkawa Sun Nuna Bacin Rai Saboda Yawaita Kashe ‘Yan Kasar Amurka
  • An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
  • Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
  • FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.