Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
Published: February 10, 2026 at 7:43 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 11, 2026

Uwargidan Gwamnan jihar Gombe, Hajiya Dakta Asma’u Inuwa Yahaya,ta jagoranci wani muhimmin taron wayar da kai da nufin ƙarfafa matakan dakilewa da kuma sauya ɗabi’un zamantakewa domin kawo ƙarshen cin zarafin mata da ‘yan mata.

An gudanar da taron ne a Cibiyar Ilimi wato (Education Resource Centre) da ke Tashan Dukku a birnin Gombe, tare da halartar jami’an gwamnati, shugabannin al’umma da na addini, ƙungiyoyin fararen hula, ƙungiyoyin mata, da kuma abokan hulɗar ci gaba.

Shirin, wanda aka aiwatar tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Matan Gwamnonin Nijeriya da kuma tallafin gidauniyar Ford Foundation, ya gudana ne ƙarƙashin taken: “Wayar da Kai don Rigakafi: Sauya Ka’idojin Zamantakewa da Ƙarfafa Ƙudurin Jiha Don Kawar da Cin Zarafin Mata.”

A jawabinta, Hajiya Dakta Asma’u Inuwa Yahaya Wacce Kwamishinar Ma’aikatar harkokin Mata Asma’u Mohammed Iganus ta wakilta ta jaddada cewa rigakafi shi ne hanya mafi tasiri wajen magance matsalar cin zarafi sannan ta bayyana cewa sauya tunani da halayen da ke goyon bayan danniya da take hakkin mata na da muhimmanci wajen gina al’umma mai adalci da mutunta juna.

Uwargidan Gwamnan ta kuma tabbatar da ƙudurin gwamnatin Jihar Gombe na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su kare haƙƙin mata da ‘yan mata, tare da samar da ingantattun hanyoyin kai ƙorafi da tallafa wa waɗanda abin ya shafa.

Masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yi kira ga haɗin kai tsakanin gwamnati, al’umma da ƙungiyoyin fararen hula domin tabbatar da cewa an kawo ƙarshen cin zarafin mata a kowane mataki. Sun kuma yabawa gwamnatin jihar bisa matakan da take ɗauka wajen ƙarfafa tsarin kariya da inganta walwalar mata da yara.

Taron ya kasance wani muhimmin mataki na ƙara wayar da kai da kuma gina aniyar haɗin gwiwa domin samar da al’umma mai zaman lafiya, adalci da mutunta haƙƙin bil’adama.

Ga Rahoton Aliyu Gerengi Gombe Daga Gombe

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/GBV-GOMBE.mp3
Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
Next Post: Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya
Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika
  • Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
  • Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu Afrika
  • Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.