Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya
Published: November 25, 2025 at 8:38 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 25, 2025

Hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ta ce hare-haren ‘yan bindiga a yankin Arewacin Najeriya zai haddasa bala’in rashin abinci da ya fi na ko’ina muni a Nahiyar Afirka a cikin shekara mai zuwa.

A wani rahoton da hukumar ta wallafa yau Talata, ta yi kiyasin cewa mutane kimanin miliyan 35 zasu iya fuskantar yunwa a Najeriya a shekara mai zuwa, wanda zai kasance shine mafi muni a duk fadin nahiyar Afirka, kuma mafi muni da za a gani a cikin Najeriya tun daga lokacin da hukumar ta fara tattara irin wadannan alkaluma.

Hukumar ta kuma ce akwai mutane kimanin dubu 15 da zasu fuskanci bala’in mummunar yunwa mai iya kaiwa ga hallaka a Jihar Borno a shekara mai zuwa. Hukumar zata dora jihar Borno a mataki na 5 na bala’in yunwa, wanda shine matakin mafi muni na rashin abinci, kamar irin yadda ake gani a Gaza da Sudan.

Hukumar, wadda ake kira WFP a takaice, ta ce yankin Arewacin Najeeriya zai fuskanci bala’in yunwa mafi muni da bai taba gani ba cikin shekaru 10, inda manoma da mazauna karkara zasu fi shan wahala.

Jami’ain suka ce hare-haren ‘yan bindiga dabam dabam sun hana manoma yin amfani da gonakinsu a Arewa, yayin da a watan Oktoba aka samu wata sabuwar kungiyar ‘yan ta’addar da ita ma ta shiga cikin Najeriya. Wannan kungiya mai suna Jama’at Nusrat al-Islam wal Muslimin, ta saba kai hare-hare a yankin bakin iyakar Nijar, Mali da Burkina Faso.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi
Next Post: Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro Labarai
Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya Afrika
Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika
  • Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
  • Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.