Jami’an yankin arewacin jihar New York sun tabbatar ranar Laraba cewa mutuwar wani ɗan gudun hijira daga Myanmar mai fama da matsalar gani ta kasance kisan kai, bayan ya ɓace na tsawon kwanaki da dama, wanda aka sako shi daga gidan yari zuwa hannun jami’an tsaron kan iyaka na Amurka.
An gano gawar Nurul Amin Shah Alam, mai shekaru 56, a kan wani titi a tsakiyar birnin Buffalo a cikin watan Fabrairu, a lokacin sanyi mai tsanani. Nurul Amin, wanda ya fito daga dangin ‘yan gudun hijirar Arakan Rohingya, ba ya jin Turanci kuma yana tafiya da sanda.
Mutuwarsa ta jawo damuwa da kuma fusata jama’a dangane da yadda ake mu’amala da baƙin haure a lokacin tsauraran matakan shige da fice na Shugaba Donald Trump. Baya ga wannan lamari na Nurul aƙalla mutane 14 sun mutu a hannun hukumomin kula da baƙin haure a shekarar 2026.


