Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai
Published: November 16, 2025 at 12:32 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Kasar Iran ta tabbatar a yau Asabar cewa dakarunta na juyin juya hali sun damke wani jirgin tanka da suka ce ya keta dokoki, wanda ke dauke da fetur a cikin tekun Gulf, wanda aka ce ya doshi kasar Singapore.

A jiya jumma’a ne jami’an Amurka da majiyoyin tsaron zirga zirgar jiragen ruwa suka ce dakarun Iran sun tare wannan jirgi suka juya akalarsa zuwa cikin yankin ruwan kasar Iran din.

Wannan shine karon farko da Iran take kama wani jirgin ruwa a cikin tekun Gulf tun cikin watan Afrilun 2024.

Gidan Talebijin na Iran ya karanta wata sanarwar da Rundunar Dakarun Juyin Juya Hali ta kasar ta bayar dake cewa,  jirgin ruwan tankar ya keta doka ta hanyar dauko kayayyakin da ba a amince da safararsu ba. Sanarwar ba ta yi karin bayani a kan wannan abu da ake zargi.

Wannan jirgin ruwan da Iran ta kama a mashigin ruwan Hormuz, ya yi lodi ne a Sharjah dake Hadaddiyar Daular Larabawa.

Iran dai ta dakile yawan ayyukanta na soja a yankin tun bayan dauki ba dadin da suka gwabza da Isra’ila da  Amurka a watan Yunin wannan shekara.

Labarai

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke
Next Post: Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere Afrika
Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai
PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Mamakon Ruwan Sama Da Iska Ya Hallaka Mutane Uku A Jihar Yobe Labarai
  • An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
  • Trump Yace Kawayen Amurka A Kungiyar NATO Basa Goyon Bayan Su Afrika
  • Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.