Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika

Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki
Published: June 7, 2026 at 1:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: June 7, 2026

Ƙungiyar likitoci masu neman kwarewa ta Nijeriya, wato Nigerian Association of Resident Doctors (NARD), ta yi barazanar shiga yajin aiki idan gwamnati ba ta ɗauki matakan da suka dace ba wajen dakile cin zarafi da ake kai wa ma’aikatan lafiya a faɗin ƙasar.

Ƙungiyar ta bayyana cewa aƙalla manyan cibiyoyin lafiya 17 sun fuskanci hare-hare kan likitoci, ma’aikatan jinya da sauran ma’aikatan lafiya cikin shekara guda da ta gabata.

Ta ce sama da kashi 90 cikin 100 na waɗanda abin ya shafa mambobinta ne, inda suka gamu da raunuka da asarar dukiya.

NARD ta ce idan har zuwa ƙarshen taronta na shekara ba a ɗauki matakai masu gamsarwa ba wajen hukunta masu aikata irin waɗannan cin zarafi ba, ba za ta iya tabbatar da zaman lafiya a fannin kiwon lafiya ba bayan taron.

Ƙungiyar ta koka da cewa galibin waɗanda aka kai wa hari suna samun wasiƙar neman afuwa kawai daga masu laifi, ba tare da an hukunta su yadda ya kamata ba. Ta kuma zargi hukumomi da gaza gurfanar da masu laifin, lamarin da ke ƙara ƙarfafa masu aikata irin waɗannan laifuka.

NARD ta ce asibitocin da ya kamata su kasance wuraren ceto rayuka suna sauyawa zuwa wuraren tashin hankali, inda cin zarafi ta baki ya rikide zuwa duka, lalata dukiyoyi, kutsawa ɗakunan hutun likitoci da kuma yi musu barazana da makamai.

Ƙungiyar ta jaddada cewa rayukan likitoci da sauran ma’aikatan lafiya suna da muhimmanci, tana mai kira ga gwamnati da hukumomin tsaro su ɗauki matakan gaggawa domin kawo ƙarshen wannan matsala.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
Anyi Asarar Biliyoyin Naira A Gobarar Kasuwar Singa Labarai
Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Addini Ko Kabilanci Basu Da Gurbi Cikin Ta’addanci Labarai
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
  • Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
  • Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
  • Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.