Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci
Published: June 6, 2026 at 4:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya taya Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Dr. Abubakar Shehu Abubakar III, murnar cika shekaru 12 da hawansa karagar mulkin kakanninsa.

A cikin sakon taya murnar da ya aike, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana Sarkin Gombe a matsayin amintaccen abokin hulɗa wajen gudanar da mulki, tabbatar da zaman lafiya da kuma bunkasa ci gaba, yana mai yabawa irin kyawawan halayen shugabanci da ya nuna tun bayan hawansa karagar mulki a shekarar 2014.

Gwamnan ya ce Mai Martaba Sarkin Gombe ya yi fice wajen jagoranci mai hangen nesa, hikima da sadaukarwa ga ci gaban al’ummarsa, lamarin da ya taimaka matuka wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban tattalin arziki a Jihar Gombe.

Ya kuma yaba wa Sarkin bisa rawar da yake takawa na uba ga al’umma, ayyukan alheri da kuma ƙoƙarinsa na kare da bunƙasa al’adun gargajiyar masarautar Gombe tare da ƙarfafa zaman tare cikin lumana tsakanin al’ummomi mabambanta da ke cikin masarautarsa da ma jihar baki ɗaya.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma jinjina wa Mai Martaban bisa jajircewarsa wajen tallafa wa harkokin ilimi da bunƙasa rayuwar al’umma, musamman shirye-shiryen da ke taimakawa yara marasa galihu wajen samun ingantaccen ilimi.

Har ila yau, ya yabawa Sarkin bisa jagorancinsa a matsayin Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya da Hakimai ta Jihar Gombe, inda ya ce hakan ya taimaka wajen ƙarfafa rawar da cibiyoyin gargajiya ke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba.

Yayin da yake taya Sarkin murnar wannan gagarumin ci gaba, Gwamna Inuwa Yahaya ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya ci gaba da ba shi lafiya, hikima da tsawon rai domin ci gaba da yi wa al’ummarsa hidima cikin nasara da albarka.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
Next Post: Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki

Karin Labarai Masu Alaka

Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki Labarai
Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya
Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba Labarai
Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
  • An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
  • Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
  • Tsarin Haraji Mai Cike Da Ayoyin Tambaya Na Shirin Fara Aiki Labarai
  • Amurka Ta Bada Tabbacin Baiwa Ukraine Tsaron Na Shekaru 15 Amurka
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.