Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci
Published: June 6, 2026 at 4:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya taya Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Dr. Abubakar Shehu Abubakar III, murnar cika shekaru 12 da hawansa karagar mulkin kakanninsa.

A cikin sakon taya murnar da ya aike, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana Sarkin Gombe a matsayin amintaccen abokin hulɗa wajen gudanar da mulki, tabbatar da zaman lafiya da kuma bunkasa ci gaba, yana mai yabawa irin kyawawan halayen shugabanci da ya nuna tun bayan hawansa karagar mulki a shekarar 2014.

Gwamnan ya ce Mai Martaba Sarkin Gombe ya yi fice wajen jagoranci mai hangen nesa, hikima da sadaukarwa ga ci gaban al’ummarsa, lamarin da ya taimaka matuka wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban tattalin arziki a Jihar Gombe.

Ya kuma yaba wa Sarkin bisa rawar da yake takawa na uba ga al’umma, ayyukan alheri da kuma ƙoƙarinsa na kare da bunƙasa al’adun gargajiyar masarautar Gombe tare da ƙarfafa zaman tare cikin lumana tsakanin al’ummomi mabambanta da ke cikin masarautarsa da ma jihar baki ɗaya.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma jinjina wa Mai Martaban bisa jajircewarsa wajen tallafa wa harkokin ilimi da bunƙasa rayuwar al’umma, musamman shirye-shiryen da ke taimakawa yara marasa galihu wajen samun ingantaccen ilimi.

Har ila yau, ya yabawa Sarkin bisa jagorancinsa a matsayin Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya da Hakimai ta Jihar Gombe, inda ya ce hakan ya taimaka wajen ƙarfafa rawar da cibiyoyin gargajiya ke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba.

Yayin da yake taya Sarkin murnar wannan gagarumin ci gaba, Gwamna Inuwa Yahaya ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya ci gaba da ba shi lafiya, hikima da tsawon rai domin ci gaba da yi wa al’ummarsa hidima cikin nasara da albarka.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
Next Post: Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki

Karin Labarai Masu Alaka

’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
An Tura Rundunar Tsaron Sham Zuwa Kakarshin Ikon Kurdawa Labarai
Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
  • Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
  • Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
  • ‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina Tsaro
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
  • SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.