Wata ’yar kasuwa a jihar Gombe ta tsallake rijiya da baya bayan wani hari da ake zargin saurayinta ya kai mata da guduma a cikin gidanta da ke unguwar Pantami a birnin Gombe.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare, lokacin da wanda ake zargin, Musa Adamu mai shekaru 35, mazaunin unguwar Riyal, ya tsallaka katangar gidan matar tare da shiga ɗakinta ba tare da izini ba.

Ana zargin ya kai mata hari da gudumar ƙarfe, sannan ya yi ƙoƙarin shaƙe ta da igiyar USB. Duk da munanan raunukan da ta samu, matar ta samu damar yin ihu domin neman taimako, lamarin da ya jawo hankalin maƙwabta tare da tilasta wa maharin tserewa daga wurin.
Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta tabbatar da kama wanda ake zargin bisa laifukan yunƙurin kisa, fashi da makami da kuma jikkata mutum.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa bayan harin, jami’an ’yan sanda sun garzaya da matar zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci, inda daga bisani aka sallame ta bayan samun sauƙi.
Binciken farko da ’yan sanda suka gudanar ya nuna cewa wanda ake zargin ya taɓa neman matar ta ba shi kuɗi, amma ta ƙi amincewa da buƙatarsa, abin da ake zargin ya haddasa sabanin da ya kai ga harin.
Rundunar ta ce ta ƙwato gudumar da ake zargin an yi amfani da ita wajen kai harin da kuma igiyar USB da ake zargin an yi ƙoƙarin amfani da ita wajen shaƙe matar.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, Umar Ahmed Chosu, ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da ɗaukar tsauraran matakai domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da cewa an hukunta masu aikata laifuka bisa doka.


