Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata
Published: June 11, 2026 at 9:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata ’yar kasuwa a jihar Gombe ta tsallake rijiya da baya bayan wani hari da ake zargin saurayinta ya kai mata da guduma a cikin gidanta da ke unguwar Pantami a birnin Gombe.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare, lokacin da wanda ake zargin, Musa Adamu mai shekaru 35, mazaunin unguwar Riyal, ya tsallaka katangar gidan matar tare da shiga ɗakinta ba tare da izini ba.

Ana zargin ya kai mata hari da gudumar ƙarfe, sannan ya yi ƙoƙarin shaƙe ta da igiyar USB. Duk da munanan raunukan da ta samu, matar ta samu damar yin ihu domin neman taimako, lamarin da ya jawo hankalin maƙwabta tare da tilasta wa maharin tserewa daga wurin.

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta tabbatar da kama wanda ake zargin bisa laifukan yunƙurin kisa, fashi da makami da kuma jikkata mutum.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa bayan harin, jami’an ’yan sanda sun garzaya da matar zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci, inda daga bisani aka sallame ta bayan samun sauƙi.

Binciken farko da ’yan sanda suka gudanar ya nuna cewa wanda ake zargin ya taɓa neman matar ta ba shi kuɗi, amma ta ƙi amincewa da buƙatarsa, abin da ake zargin ya haddasa sabanin da ya kai ga harin.

Rundunar ta ce ta ƙwato gudumar da ake zargin an yi amfani da ita wajen kai harin da kuma igiyar USB da ake zargin an yi ƙoƙarin amfani da ita wajen shaƙe matar.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, Umar Ahmed Chosu, ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da ɗaukar tsauraran matakai domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da cewa an hukunta masu aikata laifuka bisa doka.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko
Next Post: ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu

Karin Labarai Masu Alaka

Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
  • Hukumar Kare Hakkin ‘Yan Jarida Tace Isra’ila Ce Ta Kashe ‘Yan Jarida Kashi Biyu Bisa Uku Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka Amurka
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
  • Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.