Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Afrika
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis Afrika
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika

‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu
Published: June 11, 2026 at 10:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: June 11, 2026

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta fara aiwatar da wani samame na musamman kan motocin da ke zirga-zirga ba tare da lambar rijista ba ko kuma masu amfani da hanyoyin boye bayanan lambobin motocinsu.

Rundunar ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Olatunji Rilwan Disu, wanda ya bayyana cewa yawaitar motocin da ke aiki ba tare da cikakken rajista ba ko masu boye lambobin mota ya saba wa doka kuma yana barazana ga tsaro da lafiyar jama’a.

A cewarsa, rajistar mota na taka muhimmiyar rawa wajen dakile aikata laifuka, tattara bayanan sirri na tsaro da kuma saukaka ayyukan jami’an tsaro. Ya kara da cewa masu aikata laifuka kan yi amfani da motocin da ba a iya gane su wajen aikata miyagun laifuka tare da kauce wa gano su.

A cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, rundunar ta ce ta fara gudanar da sintiri da bincike a sassan jihar domin gano motocin da ba su da sahalallun lambobin rijista ko kuma wadanda aka boye lambobinsu.

Sanarwar ta yi gargadin cewa duk motar da aka samu da irin wannan laifi za a tsayar da ita, a kwace ta tare da daukar matakan shari’a da suka dace kamar yadda doka ta tanada.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, Umar Ahmed Chuso, ya bukaci masu ababen hawa su tabbatar da cewa motocinsu suna da cikakkiyar rajista tare da nuna sahalallun lambobin mota a fili a kowane lokaci.

Ya kuma gargadi masu motoci da su guji amfani da murfin lamba ko wasu gyare-gyare da ke hana ganin lambobin mota a sarari, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukuncin da doka ta tanada.

Kwamishinan ya yi kira ga duk masu amfani da hanyoyi da su bi dokokin hanya domin taimakawa kokarin gwamnati da hukumomin tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta sake tabbatar da kudurinta na ci gaba da aiwatar da dukkan matakan da suka dace wajen hana aikata laifuka da kuma tabbatar da tsaron jama’a a fadin jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: ’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Karin Labarai Masu Alaka

Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai
Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika
Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda Afrika
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • ’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.