Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika

‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu
Published: June 11, 2026 at 10:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: June 11, 2026

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta fara aiwatar da wani samame na musamman kan motocin da ke zirga-zirga ba tare da lambar rijista ba ko kuma masu amfani da hanyoyin boye bayanan lambobin motocinsu.

Rundunar ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Olatunji Rilwan Disu, wanda ya bayyana cewa yawaitar motocin da ke aiki ba tare da cikakken rajista ba ko masu boye lambobin mota ya saba wa doka kuma yana barazana ga tsaro da lafiyar jama’a.

A cewarsa, rajistar mota na taka muhimmiyar rawa wajen dakile aikata laifuka, tattara bayanan sirri na tsaro da kuma saukaka ayyukan jami’an tsaro. Ya kara da cewa masu aikata laifuka kan yi amfani da motocin da ba a iya gane su wajen aikata miyagun laifuka tare da kauce wa gano su.

A cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, rundunar ta ce ta fara gudanar da sintiri da bincike a sassan jihar domin gano motocin da ba su da sahalallun lambobin rijista ko kuma wadanda aka boye lambobinsu.

Sanarwar ta yi gargadin cewa duk motar da aka samu da irin wannan laifi za a tsayar da ita, a kwace ta tare da daukar matakan shari’a da suka dace kamar yadda doka ta tanada.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, Umar Ahmed Chuso, ya bukaci masu ababen hawa su tabbatar da cewa motocinsu suna da cikakkiyar rajista tare da nuna sahalallun lambobin mota a fili a kowane lokaci.

Ya kuma gargadi masu motoci da su guji amfani da murfin lamba ko wasu gyare-gyare da ke hana ganin lambobin mota a sarari, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukuncin da doka ta tanada.

Kwamishinan ya yi kira ga duk masu amfani da hanyoyi da su bi dokokin hanya domin taimakawa kokarin gwamnati da hukumomin tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta sake tabbatar da kudurinta na ci gaba da aiwatar da dukkan matakan da suka dace wajen hana aikata laifuka da kuma tabbatar da tsaron jama’a a fadin jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: ’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
An Kashe Sojojin Ukraine Dubu 55 A Kasar Rasha Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar Amurka
  • Ba Mamaki APC Ta Kafa Tarihi A Ranar Litinin Najeriya
  • Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
  • Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta Wasanni
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf Afrika
  • Wakilan Rasha Da Ukraine Sun Tattauna A Abu Dhabi Ranar Juma’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.