Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta fara aiwatar da wani samame na musamman kan motocin da ke zirga-zirga ba tare da lambar rijista ba ko kuma masu amfani da hanyoyin boye bayanan lambobin motocinsu.
Rundunar ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Olatunji Rilwan Disu, wanda ya bayyana cewa yawaitar motocin da ke aiki ba tare da cikakken rajista ba ko masu boye lambobin mota ya saba wa doka kuma yana barazana ga tsaro da lafiyar jama’a.
A cewarsa, rajistar mota na taka muhimmiyar rawa wajen dakile aikata laifuka, tattara bayanan sirri na tsaro da kuma saukaka ayyukan jami’an tsaro. Ya kara da cewa masu aikata laifuka kan yi amfani da motocin da ba a iya gane su wajen aikata miyagun laifuka tare da kauce wa gano su.
A cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, rundunar ta ce ta fara gudanar da sintiri da bincike a sassan jihar domin gano motocin da ba su da sahalallun lambobin rijista ko kuma wadanda aka boye lambobinsu.
Sanarwar ta yi gargadin cewa duk motar da aka samu da irin wannan laifi za a tsayar da ita, a kwace ta tare da daukar matakan shari’a da suka dace kamar yadda doka ta tanada.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, Umar Ahmed Chuso, ya bukaci masu ababen hawa su tabbatar da cewa motocinsu suna da cikakkiyar rajista tare da nuna sahalallun lambobin mota a fili a kowane lokaci.
Ya kuma gargadi masu motoci da su guji amfani da murfin lamba ko wasu gyare-gyare da ke hana ganin lambobin mota a sarari, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukuncin da doka ta tanada.
Kwamishinan ya yi kira ga duk masu amfani da hanyoyi da su bi dokokin hanya domin taimakawa kokarin gwamnati da hukumomin tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta sake tabbatar da kudurinta na ci gaba da aiwatar da dukkan matakan da suka dace wajen hana aikata laifuka da kuma tabbatar da tsaron jama’a a fadin jihar.


