Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar
Published: March 16, 2026 at 8:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jagoran ‘yan adawar Uganda Bobi Wine ya ce ya bar kasar na wani dan lokaci bayan ya shafe watanni biyu yana boye sakamakon zaben shugaban kasar da aka gudanar a watan Janairu tsakanin shi da shugab Yoweri ‌Museveni, wanda ya dade yana mulkin kasar.

Wine, wanda ainihin sunansa Robert Kyagulanyi, ya ki amincewa da sakamakon wannan zaben, yana zargin an tafka magudi, kuma ya kasance a boye tun bayan da ya tsere daga gidansa da ke Kampala babban birnin Uganda.

A cikin wani sakon bidiyo na mintuna biyar da ya wallafa shafinsa na X ranar Asabar, Wine ya ce ya bar kasar ne don “mahimman al’amura a wajen Uganda”, ba tare da bayyana inda yake ko kuma mene ne alkawuran ba.

“A lokacin da ya dace zan dawo in ci gaba da yin hakan,” in ji shi.

Tauraron mawakin nan da ya koma siyasa ya ce yakin neman zabensa na da nasaba da yadda jami’an tsaro suka hana shi gangamin tare da kame magoya bayansa.

Afrika, Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo
Next Post: Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare

Karin Labarai Masu Alaka

Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka Afrika
Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe Afrika
Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta Wasanni
  • Shugaba Trump Ya Hana Kaiwa Cuba Man Fetur Daga Venezuela Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 30 A Jihar Neja Najeriya
  • Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
  • Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
  • Asusun IMF Zasu Ziyarci Kasar Gabon Afrika
  • Sama da mutane dubu 500 ne yanbindiga suka kora daga gidajensu a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.