Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe
Published: June 20, 2026 at 7:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar ‘yan uwa Musulmi Almajiran Sayyid Ibrahim Yaqub El-Zakzaky (H) a jihar Gombe sun shiga rana ta uku na gudanar da zaman makokin Ashura, domin tunawa da shahadar Imam Hussain (AS) da iyalan gidan Manzon Allah (SAW) a filin Karbala, lamarin da ya faru a shekara ta 61 bayan hijira.

A ranar ta uku, an gudanar da wani shiri na musamman domin tunawa da Aliyul Asghar (AS), jaririn Imam Hussain (AS), wanda ya yi shahada a lokacin yaƙin Karbala.

Da yake gabatar da jawabi a wajen taron, Shugaban ‘yan uwa Musulmi a Gombe Sheikh Muhammad Abbari ya yi cikakken bayani kan yadda Aliyul Asghar ya yi shahada, tare da bayyana darussan sadaukarwa, juriya da tsayin daka da ake koya daga wannan tarihi.

Shehin malamin ya jaddada muhimmancin bin tafarkin Imam Hussain (AS) wajen kare gaskiya da adalci, yana mai kira ga mabiya da su kasance masu jajircewa a gaban zalunci da danniya.

Ya kuma yi bayani kan ƙa’idojin yaƙi a Musulunci, inda ya ce abin da aka yi wa Aliyul Asghar ya saɓa wa dokoki da ka’idojin yaƙi da addinin Musulunci ya tanada.

A yayin taron, iyaye masu jarirai sun ɗaga ‘ya’yansu a matsayin alamar tunawa da yadda Imam Hussain (AS) ya ɗaga jaririnsa a filin Karbala lokacin da yake neman a ba shi ruwa.

Mahalarta taron sun bayyana cewa wannan alama ce ta nuna biyayya ga koyarwar Imam Hussain (AS) da kuma ci gaba da bin tafarkin gwagwarmayar tabbatar da gaskiya da adalci.

An gudanar da taron cikin yanayi na jimami, addu’o’i da wa’azi, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen makokin Ashura a sassa daban-daban na jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sana'o'i, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
Next Post: Bayan Shekaru Biyar, Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Gano Motar da Aka Sace A Fatakwal

Karin Labarai Masu Alaka

Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
Bayan Rikicin Manoma Da Makiyaya, Kwamitin White Paper Ya Ziyarci Bojude Da Kwami Afrika
Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa Afrika
Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC Siyasa
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
  • Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia Tsaro
  • Layin Raba Wutan Lantarki Na Najeriya Ya Fashe Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.