Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika

Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe
Published: June 20, 2026 at 7:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar ‘yan uwa Musulmi Almajiran Sayyid Ibrahim Yaqub El-Zakzaky (H) a jihar Gombe sun shiga rana ta uku na gudanar da zaman makokin Ashura, domin tunawa da shahadar Imam Hussain (AS) da iyalan gidan Manzon Allah (SAW) a filin Karbala, lamarin da ya faru a shekara ta 61 bayan hijira.

A ranar ta uku, an gudanar da wani shiri na musamman domin tunawa da Aliyul Asghar (AS), jaririn Imam Hussain (AS), wanda ya yi shahada a lokacin yaƙin Karbala.

Da yake gabatar da jawabi a wajen taron, Shugaban ‘yan uwa Musulmi a Gombe Sheikh Muhammad Abbari ya yi cikakken bayani kan yadda Aliyul Asghar ya yi shahada, tare da bayyana darussan sadaukarwa, juriya da tsayin daka da ake koya daga wannan tarihi.

Shehin malamin ya jaddada muhimmancin bin tafarkin Imam Hussain (AS) wajen kare gaskiya da adalci, yana mai kira ga mabiya da su kasance masu jajircewa a gaban zalunci da danniya.

Ya kuma yi bayani kan ƙa’idojin yaƙi a Musulunci, inda ya ce abin da aka yi wa Aliyul Asghar ya saɓa wa dokoki da ka’idojin yaƙi da addinin Musulunci ya tanada.

A yayin taron, iyaye masu jarirai sun ɗaga ‘ya’yansu a matsayin alamar tunawa da yadda Imam Hussain (AS) ya ɗaga jaririnsa a filin Karbala lokacin da yake neman a ba shi ruwa.

Mahalarta taron sun bayyana cewa wannan alama ce ta nuna biyayya ga koyarwar Imam Hussain (AS) da kuma ci gaba da bin tafarkin gwagwarmayar tabbatar da gaskiya da adalci.

An gudanar da taron cikin yanayi na jimami, addu’o’i da wa’azi, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen makokin Ashura a sassa daban-daban na jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sana'o'i, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya

Karin Labarai Masu Alaka

Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya
Ana Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Djibouti Yau Juma’a Afrika
Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25 Shirye-Shirye
  • Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.