Gwamnan jihar Gombe kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF), Muhammadu Inuwa Yahaya, ya taya al’ummar Musulmi a Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya, har ma da sauran Musulmi a faɗin duniya, murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1448 Bayan Hijira (AH).
A cikin saƙon taya murna da ya fitar domin bikin sabuwar shekarar Hijira, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana farkon sabuwar shekarar Hijira a matsayin lokaci na sabunta ruhi, yin nazari mai zurfi kan rayuwa da kuma ƙara jajircewa wajen bin koyarwar addini, zaman lafiya, tausayi da yi wa bil’adama hidima.
Gwamnan ya ce sabuwar shekarar Musulunci wata dama ce ga al’ummar Musulmi domin su yi waiwaye kan abubuwan da suka gabata, su ɗauki darussa daga gare su sannan su fuskanci gaba da ƙarin imani, fata da ƙuduri.
Ya ce, “Yayin da muke shiga sabuwar shekarar Hijira, ya kamata mu ƙara rungumar kyawawan ɗabi’u na haƙuri, sadaukarwa, juriya da adalci waɗanda Ma’aiki Mai Tsira Annabi Muhammad (SAW) ya nuna a lokacin Hijira.”
Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Musulmi da su yi amfani da wannan wata mai alfarma na Muharram da sauran watannin da ke gaba wajen ƙara yawaita addu’o’i domin samun ɗorewar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba a Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.
Har ila yau, ya yi kira da a yi addu’o’i na musamman domin samun wadataccen ruwan sama da kuma nasarar kakar noma, yana mai bayyana fatan cewa sabuwar shekarar za ta zo da ƙarin ci gaba da damammaki ga al’umma.
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa ya kuma jaddada muhimmancin zaman lafiya tsakanin al’umma, girmama juna da haɗin kai tsakanin kabilu da addinai daban-daban a jihar da ƙasa baki ɗaya, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar ƙalubalen tsaro a wasu sassan ƙasar.
Gwamna Inuwa Yahaya ya sake tabbatar da aniyar gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da manufofi da ayyukan raya ƙasa da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar jama’a domin inganta walwala da yanayin rayuwarsu.
Ya kuma buƙaci al’umma da su kasance masu bin doka, masu tsayawa kan koyarwar addini da kuma jajircewa wajen gina al’umma mai zaman lafiya, tsaro da ci gaba.
A ƙarshe, Gwamnan ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya sanya sabuwar shekarar Musulunci ta kasance mai cike da zaman lafiya, ci gaba da rahama ga jihar Gombe, Arewacin Najeriya da ƙasar baki ɗaya.


