Shugaban jamhuriyar Dimokraɗiyyar kwango ya canza shugabancin hukumar kula da ma’adinai na kasar, kamar yadda gwamnatin ta bada sanarwa ranar Litinin, wannan gagarumin garambawul ne a dai dai lokacin da shawarwari da Amurka dangane ma’dinan kasar suke kankama.
Wani babban jami’in gwamnatin kasar Deogratias Ngele Masudi, zai karbi shugabancin hukumar, yayinda Baraka Kabemba, zai zama shugaban gudanarwa mai cikakken iko, kamar yadda sanarwar gwamnati da aka karanta a tashar talabijin ta kasar.
Tsohon shugaban hukumar kula da harkokin ma’adinan Guy Robert Lukama, yanzu shine shugaban kamfanin hakar zinari na kasar, kamar yadda sanarwar ta fada.
Nan take dai babu cikakken bayani ko wannan garambawul da gwamnati tayi yana da wata nasaba da yunkurin da gwamnatin Kwangon take yi na shawo kan Amurka ta sa kasashen yammaci su Zuba jari a bangaren ma’adinai karkashin yarjejeniya da kasashen biyu suka kulla, wadda tayi tanadi ga kasar game da tsaro.


