Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata
Published: January 10, 2026 at 7:26 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 11, 2026

Gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin fara aiwatar da manufar “Ba Aiki, Ba Albashi” kan mambobin JOHESU da ke ci gaba da yajin aiki tun daga ranar 14 ga Nuwamba, 2025.

Umarnin ya fito ne ta cikin wata takarda da ma’aikatar kafiya ta tarayya ta fitar a Abuja, wadda aka aikawa da shugabannin asibitocin tarayya, kuma zai fara aiki daga Janairu 2026.

Ma’aikatar ta ce dole ne asibitoci su tabbatar da bin dokar tare da ci gaba da bayar da muhimman ayyukan lafiya kamar kulawar gaggawa, dakunan haihuwa da sashin ICU, har ma da daukar ma’aikatan wucin gadi idan ya zama dole.

Haka kuma, an umurci asibitoci da su bar duk ma’aikatan da ke son ci gaba da aiki su yi hakan ba tare da tsangwama ba, tare da tabbatar da tsaro da aika rahotanni kan tasirin yajin aikin.

Wani kwararre a fannin lafiyar jama’a, Dr. Gabriel Adakole, ya ce duk da cewa matakin yana da tushe a doka kuma na iya kawo karshen yajin aikin, zai iya kara raunana tsarin kiwon lafiyar Najeriya, ganin muhimmancin rawar da mambobin JOHESU ke takawa a asibitoci.

Ya kara da cewa marasa lafiya ne za su fi shan wahala sakamakon jinkirin jinya da raguwar samun kulawar lafiya, yana mai kira da a yi amfani da tattaunawa da saka jari domin samar da dorewar zaman lafiya a bangaren kiwon lafiya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026
Next Post: Wikki Tourist FC: Ta Sallami ‘Yan Wasa Hudu

Karin Labarai Masu Alaka

Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko Afrika
Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe Afrika
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka
  • Ƙungiyar Mata Sunyi Kira Ga Jam’iyar P R P Da Ta Dauki Baheejja A Matsayin Mataimakiyar Gwamnan A Bauchi 2027 Labarai
  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai Wasanni
  • Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
  • Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
  • Rasha Na Cigaba Da Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Ga Ukrain Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.