Wani fitaccen jami’in difilomasiyya daga Belgium, wadda kotu ta bada umarnin a gurfanar da shi kan zargin yana da hanu a kisan Prime Ministan Kwango na farko Patrick Lumumba a shekarar 1961, ya daukaka kara, kamar yadda lauyansa ya gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters a ranar jumma’a.
Wata kotu a Belgium ce ta bada umarnin a hukunta tsohon jami’in difilomasiyyan dan shekaru 93 da haifuwa Etienne Davignon, wanda tsohon jami’in Kungiyar tarayyar turai ne ya gurfana kan zargin ya taka rawa a kisan marigayi tsohon Prime Ministan Kwango na farkon shekaru 65 da suka wuce.
Banda cewa ya daukaka kara, lauyan Etienne bai kara wani bayani ba.


