Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Kakaba Takunkumi Ga Kwamandojin Yakin Kasar Sudan
Published: February 20, 2026 at 12:36 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar Alhamis, Amurka ta aza takunkumi kan kwamandoji 3 na dakarun wucin gadi a Sudan da aka fi sani da lakabin RSF a takaice, saboda rawar da suka taka kan kawanya ko zobe da suka yi wa birnin al-Fashir na tsawon shekara daya da rabi, daga bisani suka kama birnin, tana zargin su da kashe kashe masu yawan gaske.

A cikin sanarwa da Baitul Malin Amurka ta bayar Tace an aza takunkumin, ta zargi mayakan na RSF da kisan kare dangi, cin zarafin mutane, da kuma tursasa mata da lalata, a zamanin da suka yi wa birnin al-Fashir kawanya kamin daga bisani su kama birnin cikin watan oktoban bara.

Ma’aikatar kudin na Amurka ta zargi ‘yan tawayen da boye shaidar munanan ayyukan halaka rayuka da suka yi ta wajen binne binne da kuma kone kone na dubban gawarwaki.

“Amurka tana kira ga mayakan RSF su amince da tsagaita wuta na jinkai ba tare da wani bata lokaci ba. Ba zamu lamunta da ci gaba da ruruta tarzoma ba, da kashe kashen rayuka maras ma’ana a Sudan,” ministan kudin Amurka Scott Bessent ya fada a cikin sanarwar.

Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi
Next Post: Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika
Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran Afrika
Farashin Mai Ya Ragu A Kasuwar Duniya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
  • Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki Labarai
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
  • Hukumar Zaben Najeriya Ta Sanar Da Ranar Zaben Shugaban Kasa Labarai
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Rundunar Sojin KTK Ta Harba Makami Teku Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.