Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan
Published: February 20, 2026 at 1:02 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Amurka Donald Trump, ya fadawa taron farko na kwamitin wanzar da zaman lafiya da ya kafa a ranar Alhamis cewa, kasashe da suke cikin kwamitin sun bada gudumawar kudi dala bilyan bakwai 7, domin sake gine Gaza da zarar Hamas ta kwance damara, burin na ajiya makamai tabbatarsa zai yi wuyan gaske.

Tilas ta Hamas ta ajiye makamanta da janyewar sojojin Isra’ila daga zirin, yawan kudaden da aka tara domin aikin sake gine zirin, da tura kayan agaji ga mazauna yankin da yakin ya daidaita su, sune batutuwa da za su zamo zakaran gwajin dafi na tasirin wannan kwamiti.

A jawabinsa mai tsawo, shugaba Trump ya sanar da wakilan kasashe 47 da suka halarci zaman kwamitin cewa, Amurka zata bada gudumawar kudi dala bilyan 10 ga ayyukan kwamitin wanzar da zaman lafiyan.

Shugaban na Amurka yace kungiyar kwallon kafa ta duniya FIFA zata tara kudi dala milyan 75 domin raya kwallon kafa a Gaza, yayinda MDD zata bada gudunmawar dala bilyan biyu domin ayyukan raya al’uma.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Kakaba Takunkumi Ga Kwamandojin Yakin Kasar Sudan
Next Post: Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • Kasuwannin Hannayen Jari Suna Fuskantar Durkushewa Sakamakon Matsin Lambar Shugaba Trump Amurka
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
  • Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
  • Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.