Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Shirin Kwace Iyakar Greenland Da Shugaba Trump Yakeyi Yabawa Kasashen Turai Mamaki
Published: January 20, 2026 at 9:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabannin kasashen turai da take-taken shugaban Amurka Donald Trump ta girgiza su, suna kokarin nuna hadin kai a taron shekara shekara kan tattalin arziki da harkokin duniya a Davos na kasar Switzeland, a dai dai lokacin da manyan ‘yan kasuwa a turai suke gargadin kada a biye wa zuciya wajen maida martani kan burin shugaba Trump game da tsibirin Greenland.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron, yace kada turai ta amince da “rayuwa ta mai karfi,” yace abun takaici ne wai har turai tana jan kafa wajen amfani da “dokar hana tursasawa” kan Amurka.

Mun yarda muna bukatar habaka tattalin arziki, muna bukatar daidaituwar al’amura a duniyan nan, amma muna bukatar mutunci, ba biyayya ga ‘yan cin-zali-ba.” Macron ya fadawa taron na shekara shekara, kwana daya kamin zuwan shugaban Amurka Donald Trump a zauren taron.

Ba tare da ta ambaci sunan Trump kai tsaye ba, shugabar hukumar tarayyar turai, Ursula Von der Leyen, ta bayyana bukatar tarayyar turai ta maida martani kan canji cikin gaggawa da yake wakana a duniya, tana mai cewa, lamarin yasa turai tayi ittifaki na zama mai ‘yancin kai.

“Lokaci yayi da zamu yi amfani da wannan dama, wajen gina turai mai cin gashin kai,” Vonder Leyen ta fada a cikin jawabinta.

PM Belgium, Bart De Wever, yace lokaci yayi da kungiyar tarayyar turai mai wakilai 27, zata hada kai ta gayawa shugaba Trump yana neman wuce gona da iri. Ko mu hada kai mu tsira tare, ko kuma mu ci gaba da zama a wargaje, Wever ya fada a wata tattaunawa da aka yi a wajen taron da ake yi a Davos.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana
Next Post: Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika
Shugaba Trump Ya Kara Matsin Lamba Kan Iran Amurka
Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • CP Chuso Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Gwiwar Hukumomin Tsaro A Gombe Afrika
  • Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
  • ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
  • RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur Afrika
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya Afrika
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.