Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur
Published: December 3, 2025 at 8:21 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 3, 2025

Shaidun gani da ido, da ma’aikatan agaji da kuma kwararru sun yi zargin cewa rundunar sojojin wucin gadi ta RSF ta kasar Sudan, tana yin garkuwa da mazauna wuraren da ta kama a yankin Darfur tana neman sai ‘yan’uwansu sun biya diyya kafin ta sake su.

Shaidun suka ce wadanda suka kasa biya, ana kashe su, ko a lakkada musu mummunar duka.

Babu tabbas na yawan mutanen da rundunar ta RSF take rike da su a bayan da ta kama al-Fasher, babban birnin Darfur ta Arewa a karshen watan Oktoba, amma an ce ana tsare da su a wurare dabam-dabam a sansanoni da kauyuka da dama dake yanki mai fadin kilomita 80 daga birnin, yayin da wasu ma an maida su cikin al-Fasher ana neman dubban daloli daga hannun ‘yan’uwansu.

Wadanda suka tsira da yawa da suka yi hira da Reuters sun ce ana tilasta ma ‘yan’uwanssu biyan abinda ya kama daga Fam miliyan 5 zuwa fam miliyan 60 na kudin kasar Sudan, kimanin Naira miliyan biyu zuwa miliyan 25 a kudin Najeriya, kafin a sake su, wanda kudi ne mai tsananin yawa a wannan kasa mai fama da talauci.

Wasu shaidu su 11 sun ce wadanda suka kasa biya, ana tattara su a bindige, ko a yi musu mummunar duka. Wani da ya iya samu ya biya ya kubutar da kansa, Mohammed Isma’ila, ya ce ana ba mutum kwana uku ko hudu, idan har ba a aika musu da kudin ba, sai su kashe mutum.

Yace shi da wani dan’uwansa sun tsere daga al_Fasher, amma dakarun RSF suka kama su a wani kauye kuma kowannensu sai da ya biya fam miliyan 10 na kudin Sudan, kimanin Naira miliyan hurhudu, kafin aka sake su.

Da aka nemi jin ta bakinsa, mai ba rundunar RSF shawara kan harkokin shari’a, Mohammed Mukhtar yace, wata kungiya mai adawa da tasu ce da take shigar burtu a matsayin RSF take gudanar da akasarin wannan aiki na kama mutane don neman kudin fansa a ciki da wajen birnin al-Fasher.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza
Next Post: Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya Afrika
Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza Afrika
Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Addini Ko Kabilanci Basu Da Gurbi Cikin Ta’addanci Labarai
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
  • ‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.