Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi
Published: January 22, 2026 at 11:33 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 22, 2026

Kwamitin Gudanarwar Hukumar Hajji ta Najeriya Ya Shigar da Ƙorafi ga Tinubu, Ya Nemi A Sauke Shugaban Hukumar Bisa Zargin Cin Hanci da Rashawa

Mambobin kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) sun rubuta wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu wasiƙa, suna neman a sauke shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman (Pakistan), bisa zargin cin hanci da rashawa, rashin ƙwarewa da cin zarafin mukami.

Wasiƙar, mai kwanan wata 19 ga Janairu, 2026, ta nuna cewa zarge-zargen sun haɗa da kashe kuɗaɗe ba tare da amincewar kwamitin ba, bayar da kwangiloli ba tare da bin dokokin BPP ba, da kuma karya ƙa’idojin tafiyar da harkokin kuɗi. Kwamitin ya kuma ce shugaban yana ƙarƙashin binciken EFCC.

Mambobin sun ce waɗannan matsaloli sun janyo raguwar amincewa da hukumar, tare da haifar da rashin jituwa da Masarautar Saudiyya, wanda hakan ya sa aka rage yawan maniyyatan Najeriya daga 95,000 a 2025 zuwa 50,000 a Hajjin 2026.

Kwamitin ya bayyana cewa ci gaba da barin Farfesa Usman a mukami na iya kawo cikas ga shirye-shiryen Hajji mai zuwa, tare da jefa Najeriya cikin haɗarin aiki da diflomasiyya.

Ƙoƙarin jin ta bakin sa ya ci tura, sai dai a baya ya ce koke-koken da ake yi a kansa suna da nasaba da hassada a cikin hukumar.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kasar China Ta Daina Bada Bashi Da Dalar Amurka Sai Da Kudin Kasar Yuan
Next Post: Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC

Karin Labarai Masu Alaka

Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
NSCIA Ta Gargadi Gwamnati Kan Zargin Tauye Haƙƙin Musulmi Afrika
Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko Afrika
2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
UPF Ta Bukaci Haɗin Gwiwa Da NERDC Domin Gina Al’umma Mai Zaman Lafiya Afrika
Shari’ar Abubakar Malami Ta Kaura Zuwa Sabon Alkali Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
  • INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
  • An Tura Rundunar Tsaron Sham Zuwa Kakarshin Ikon Kurdawa Labarai
  • Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.