Daga cikin matakan da hukumomin tsaro ke dauka na dakile ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya, dakarun sojin Najeriya tare da hadin gwiwar sojojin Amurka sun kai wani gagarumin samame kan maboyar mayakan kungiyar IS a yankin Tafkin Chadi, lamarin da ya yi sanadin hallaka babban jagoransu da ake nema ruwa a jallo, Abu-Bilal Al-Manuki, wanda aka fi sani da Abu-Mainok.
Rahotanni sun ce an gudanar da harin ne a daren jiya bayan samun bayanan sirri da suka nuna inda jagoran kungiyar da wasu manyan kwamandojinsa suke boye.
Majiyoyi sun bayyana cewa samamen ya kuma yi sanadin kashe wasu daga cikin na hannun damansa tare da lalata sansanonin da ake zargin kungiyar na amfani da su wajen tsara hare-hare a yankin Tafkin Chadi da wasu sassan Arewa maso Gabas.
An ce aikin hadin gwiwar ya gudana cikin kwarewa, inda aka yi amfani da bayanan leken asiri da kuma kayan aiki na zamani wajen kai harin ba tare da bata lokaci ba.
Da yake mayar da martani kan nasarar aikin, Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yabawa hadin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka, yana mai cewa hakan na nuna muhimmancin zumuncin kasashen biyu wajen yaki da ta’addanci.
“Ina mika godiyata ta musamman ga Shugaba Donald Trump saboda jagorancinsa da kuma goyon bayan da Amurka ke bai wa Najeriya a wannan fafutuka,” in ji shugaban.
Tinubu ya kuma jinjinawa dakarun da suka gudanar da aikin daga bangarorin biyu saboda bajinta da kwarewar da suka nuna wajen aiwatar da samamen.
“Munanan hare-hare irin wannan su ci gaba da fadawa maboyar ‘yan ta’adda a duk inda suke a fadin kasar nan,” in ji shi.
Masana harkokin tsaro na ganin hallaka Abu-Bilal Al-Manuki na iya zama babbar koma baya ga ayyukan kungiyar IS a yankin Tafkin Chadi, musamman ganin yadda ake alakanta shi da shirya hare-hare da safarar makamai a tsakanin kasashen yankin.
A ‘yan shekarun baya-bayan nan, Najeriya ta kara karfafa hadin gwiwar tsaro da kasashen duniya domin dakile matsalar ta’addanci da ta addabi wasu sassan kasar, musamman Arewa maso Gabas.


