Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
Published: May 16, 2026 at 7:54 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Daga cikin matakan da hukumomin tsaro ke dauka na dakile ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya, dakarun sojin Najeriya tare da hadin gwiwar sojojin Amurka sun kai wani gagarumin samame kan maboyar mayakan kungiyar IS a yankin Tafkin Chadi, lamarin da ya yi sanadin hallaka babban jagoransu da ake nema ruwa a jallo, Abu-Bilal Al-Manuki, wanda aka fi sani da Abu-Mainok.

Rahotanni sun ce an gudanar da harin ne a daren jiya bayan samun bayanan sirri da suka nuna inda jagoran kungiyar da wasu manyan kwamandojinsa suke boye.

Majiyoyi sun bayyana cewa samamen ya kuma yi sanadin kashe wasu daga cikin na hannun damansa tare da lalata sansanonin da ake zargin kungiyar na amfani da su wajen tsara hare-hare a yankin Tafkin Chadi da wasu sassan Arewa maso Gabas.

An ce aikin hadin gwiwar ya gudana cikin kwarewa, inda aka yi amfani da bayanan leken asiri da kuma kayan aiki na zamani wajen kai harin ba tare da bata lokaci ba.

Da yake mayar da martani kan nasarar aikin, Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yabawa hadin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka, yana mai cewa hakan na nuna muhimmancin zumuncin kasashen biyu wajen yaki da ta’addanci.

“Ina mika godiyata ta musamman ga Shugaba Donald Trump saboda jagorancinsa da kuma goyon bayan da Amurka ke bai wa Najeriya a wannan fafutuka,” in ji shugaban.

Tinubu ya kuma jinjinawa dakarun da suka gudanar da aikin daga bangarorin biyu saboda bajinta da kwarewar da suka nuna wajen aiwatar da samamen.

“Munanan hare-hare irin wannan su ci gaba da fadawa maboyar ‘yan ta’adda a duk inda suke a fadin kasar nan,” in ji shi.

Masana harkokin tsaro na ganin hallaka Abu-Bilal Al-Manuki na iya zama babbar koma baya ga ayyukan kungiyar IS a yankin Tafkin Chadi, musamman ganin yadda ake alakanta shi da shirya hare-hare da safarar makamai a tsakanin kasashen yankin.

A ‘yan shekarun baya-bayan nan, Najeriya ta kara karfafa hadin gwiwar tsaro da kasashen duniya domin dakile matsalar ta’addanci da ta addabi wasu sassan kasar, musamman Arewa maso Gabas.

Afrika, Amurka, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
Next Post: Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Bada Tabbacin Baiwa Ukraine Tsaron Na Shekaru 15 Amurka
Amurka Ta Girke Jirage Marasa Matuki Tare Da Sojoji A Najeriya Afrika
Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
Yayale Ahmed Ya Jagoranci Kwamitin Amintattu Na Asusun Tsaron Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sun Kaddamar da Kwamitin Asusun Tsaro Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.