Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika

Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
Published: May 16, 2026 at 2:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya halarci zaɓen fidda gwani na ƴan majalisan wakilai na Jam’iyyar APC da aka gudanar a gundumar Jekadafari dake Ƙaramar Hukumar Gombe, inda ya yaba da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali a faɗin jihar Gombe.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan zaɓen, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana gamsuwa da yadda ƴan jam’iyyar suka fito, da kuma yadda aka gudanar da zaɓen cikin tsari a duk faɗin jihar.

Gwamnan, wanda ya yi matuƙar farin ciki, ya yabawa kwamitin gudanar da zaɓen da dukkan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar saboda tabbatar da ingantaccen tsari, zaman lafiya da sahihanci wanda ya bai wa duk masu sha’awar takara damar taka rawar gaban hantsi.

“Dukkanmu iyali ɗaya ne, kuma babu wanda ya yi nasara, babu wanda ya faɗi. A ganina, dukkansu ‘yan APC ne kuma ina ƙira ga kowa a haɗa kai don samun nasarar jam’iyyarmu a babban zaɓe mai zuwa,” in ji shi.

Ya kuma jaddada buƙatar haɗa kai wajen ci gaba da ayyukan gina jam’iyyar APC a Jihar Gombe.

Gwamnan ya ƙara da cewa, “Za mu ci gaba da aiki tare don cimma buri da muradun al’ummar jihar Gombe.”

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma nuna farin ciki da yadda ƴan jam’iyyar suka nuna dottaku da sanin ya kamata, yana mai cewa rungumar ɗabi’un demokraɗiyya cikin lumana alama ce mai kyau ga makomar jihar da jam’iyyar.

“Ina farin ciki da ganin yadda jama’a suka rungumi demokraɗiyya kuma suna aiwatar da ita cikin lumana,” in ji shi.

Shi ma da yake jawabi, wakilin uwar Jam’iyyar APC ta ƙasa kuma shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na jihar Gombe, Alhaji Labiru Musa Ƙafur, ya yabawa jam’iyyar reshen Jihar Gombe a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Inuwa Yahaya saboda ɗaukaka manufofin demokraɗiyya da kuma ƙarfafa demokraɗiyyar cikin gida.

“Mun gamsu sosai da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da kuma yadda aka gudanar da shi cikin gaskiya da adalci,” in ji shi.

Jami’an INEC da masu sanya ido masu zaman kansu ne suka bibiyi yadda zaben fidda gwanin ya gudana.

Masu neman tsayawa takarar kujerar Majalisar Tarayya na Gombe/ Kwami/Funakaye; Hon. Sadam Bello da Alhaji Zakariyya Jidda sun samu wakilcin wakilansu, yayin da jagoran zaɓen na gundumar Alhaji Yahaya Ibrahim Maƙeri bayan ya kammala ƙidayan ƙuri’u ya bayyana Sadam Bello a matsayin wanda ya lashe zaɓen a gundumar Jekadafari.

Haka dai lamarin ya kasance a sauran gundumomi daban-daban a jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
Next Post: Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
  • Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran Labarai
  • Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.