Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
Published: May 16, 2026 at 2:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya halarci zaɓen fidda gwani na ƴan majalisan wakilai na Jam’iyyar APC da aka gudanar a gundumar Jekadafari dake Ƙaramar Hukumar Gombe, inda ya yaba da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali a faɗin jihar Gombe.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan zaɓen, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana gamsuwa da yadda ƴan jam’iyyar suka fito, da kuma yadda aka gudanar da zaɓen cikin tsari a duk faɗin jihar.

Gwamnan, wanda ya yi matuƙar farin ciki, ya yabawa kwamitin gudanar da zaɓen da dukkan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar saboda tabbatar da ingantaccen tsari, zaman lafiya da sahihanci wanda ya bai wa duk masu sha’awar takara damar taka rawar gaban hantsi.

“Dukkanmu iyali ɗaya ne, kuma babu wanda ya yi nasara, babu wanda ya faɗi. A ganina, dukkansu ‘yan APC ne kuma ina ƙira ga kowa a haɗa kai don samun nasarar jam’iyyarmu a babban zaɓe mai zuwa,” in ji shi.

Ya kuma jaddada buƙatar haɗa kai wajen ci gaba da ayyukan gina jam’iyyar APC a Jihar Gombe.

Gwamnan ya ƙara da cewa, “Za mu ci gaba da aiki tare don cimma buri da muradun al’ummar jihar Gombe.”

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma nuna farin ciki da yadda ƴan jam’iyyar suka nuna dottaku da sanin ya kamata, yana mai cewa rungumar ɗabi’un demokraɗiyya cikin lumana alama ce mai kyau ga makomar jihar da jam’iyyar.

“Ina farin ciki da ganin yadda jama’a suka rungumi demokraɗiyya kuma suna aiwatar da ita cikin lumana,” in ji shi.

Shi ma da yake jawabi, wakilin uwar Jam’iyyar APC ta ƙasa kuma shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na jihar Gombe, Alhaji Labiru Musa Ƙafur, ya yabawa jam’iyyar reshen Jihar Gombe a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Inuwa Yahaya saboda ɗaukaka manufofin demokraɗiyya da kuma ƙarfafa demokraɗiyyar cikin gida.

“Mun gamsu sosai da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da kuma yadda aka gudanar da shi cikin gaskiya da adalci,” in ji shi.

Jami’an INEC da masu sanya ido masu zaman kansu ne suka bibiyi yadda zaben fidda gwanin ya gudana.

Masu neman tsayawa takarar kujerar Majalisar Tarayya na Gombe/ Kwami/Funakaye; Hon. Sadam Bello da Alhaji Zakariyya Jidda sun samu wakilcin wakilansu, yayin da jagoran zaɓen na gundumar Alhaji Yahaya Ibrahim Maƙeri bayan ya kammala ƙidayan ƙuri’u ya bayyana Sadam Bello a matsayin wanda ya lashe zaɓen a gundumar Jekadafari.

Haka dai lamarin ya kasance a sauran gundumomi daban-daban a jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
Next Post: Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar Afrika
Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta Kimiya
Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Idan Allah Yasa Muka Kafa Gwamnati Zamu Kyautata Wa Ma’aikata Yakubu Adamu Dan Takarar Kujeran Gwamnan Bauchi Labarai
  • Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
  • Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
  • Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.