Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya halarci zaɓen fidda gwani na ƴan majalisan wakilai na Jam’iyyar APC da aka gudanar a gundumar Jekadafari dake Ƙaramar Hukumar Gombe, inda ya yaba da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali a faɗin jihar Gombe.
Da yake jawabi jim kaɗan bayan zaɓen, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana gamsuwa da yadda ƴan jam’iyyar suka fito, da kuma yadda aka gudanar da zaɓen cikin tsari a duk faɗin jihar.

Gwamnan, wanda ya yi matuƙar farin ciki, ya yabawa kwamitin gudanar da zaɓen da dukkan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar saboda tabbatar da ingantaccen tsari, zaman lafiya da sahihanci wanda ya bai wa duk masu sha’awar takara damar taka rawar gaban hantsi.
“Dukkanmu iyali ɗaya ne, kuma babu wanda ya yi nasara, babu wanda ya faɗi. A ganina, dukkansu ‘yan APC ne kuma ina ƙira ga kowa a haɗa kai don samun nasarar jam’iyyarmu a babban zaɓe mai zuwa,” in ji shi.
Ya kuma jaddada buƙatar haɗa kai wajen ci gaba da ayyukan gina jam’iyyar APC a Jihar Gombe.
Gwamnan ya ƙara da cewa, “Za mu ci gaba da aiki tare don cimma buri da muradun al’ummar jihar Gombe.”

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma nuna farin ciki da yadda ƴan jam’iyyar suka nuna dottaku da sanin ya kamata, yana mai cewa rungumar ɗabi’un demokraɗiyya cikin lumana alama ce mai kyau ga makomar jihar da jam’iyyar.
“Ina farin ciki da ganin yadda jama’a suka rungumi demokraɗiyya kuma suna aiwatar da ita cikin lumana,” in ji shi.
Shi ma da yake jawabi, wakilin uwar Jam’iyyar APC ta ƙasa kuma shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na jihar Gombe, Alhaji Labiru Musa Ƙafur, ya yabawa jam’iyyar reshen Jihar Gombe a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Inuwa Yahaya saboda ɗaukaka manufofin demokraɗiyya da kuma ƙarfafa demokraɗiyyar cikin gida.

“Mun gamsu sosai da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da kuma yadda aka gudanar da shi cikin gaskiya da adalci,” in ji shi.
Jami’an INEC da masu sanya ido masu zaman kansu ne suka bibiyi yadda zaben fidda gwanin ya gudana.
Masu neman tsayawa takarar kujerar Majalisar Tarayya na Gombe/ Kwami/Funakaye; Hon. Sadam Bello da Alhaji Zakariyya Jidda sun samu wakilcin wakilansu, yayin da jagoran zaɓen na gundumar Alhaji Yahaya Ibrahim Maƙeri bayan ya kammala ƙidayan ƙuri’u ya bayyana Sadam Bello a matsayin wanda ya lashe zaɓen a gundumar Jekadafari.
Haka dai lamarin ya kasance a sauran gundumomi daban-daban a jihar.


