Tsarin shirin bada tallafin abinci na Majalisar Dinkin Duniya ya ce abincin da ya ke kaiwa kasar Somalia don ceto mutanen kasar daga kangin yunwa Zai iya tsayawa cak nan da zuwa watan Afrilu, idan ba’a samu kudaden da za’a ci gaba da bada tallafin ba, abinda ka iya jefa miliyoyin mutane cikin halin ha’ula’i na yunwa.
A kalla mutane miliyan hudu da dubu dari hudu ne suke fuskantar rashin abinci, inda kusan miliyan daya daga cikin su suke fuskantar matsananciyar yunwa saboda rashin samun wadataccen ruwan sama, yaki, da kuma raguwar kudaden taimako.
Shugaban shiri da bada agajin gaggawa, Ross Smith, ya ce abun ya yi munin da, mutane da dama sun rasa komai nasu, ya ce idan ba’a kawo daukin abinci da gaggawa ba, abun zai kara kwabewa.


