Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran
Published: March 27, 2026 at 6:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Amurka Donlad Trump ya ce ‘yan kasar Iran, mutane ne da suka kware wajen tattaunawa kan cimma yarjejeniya, amma ya kara da cewa baya zaton zai yi wata yarjejeniya da su don kawo karshen yakin da Isra’ila da Amurka suke yi da Iran din.

Da yake magana yayin wata tattaunawa da majalisar ministoci a fadar White house, Trum yace yanzu Iran na da damar soke duk wani kudiri nasu na makamashin nukiliya har abada, su sauya manufa. Ya kara da cewa zamu ga idan suna so suyi hakan, idan kuma sun ki, zamu zame musu karfen kafa, mu ci gaba da aika musu da bama bamai.

Jawabin na Trump yayi biyo bayan matsin rayuwa da sanadin yakin ya jawo ke kara tsamari, inda ake fuskantar rashin isasshen man fetur da gas, abinda ya sa kamfanoni da kasashe tashi tsaye wajen kokarin shawo kan lamarin.

Jakadan Amurka na musamman, Steve Witkoff ya tabbatar da cewa Amurka ta aike da takarda mai dauke da ka’idoji 15, a matsayin hanyar da za’a bi don tattaunawa kan kawo karshen yakin, ya kara da cewa akwai alama cewa fadar gwamnatin Tehran nada sha’awar cimma yarjejeniya.

Ministan harkokin waje na kasar Pakistan yace tattaunawa tsakanin Amurka da iran na wanzuwa ne ta hanyar sakonni da ake aikowa ta hannun fadar gwamnatin Islamabad, tare da wasu kasashe da suka hada da Turkiyya da Masar, wanda suma suke goyon bayan tattaunawar sulhu.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta
Next Post: Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji Afrika
Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
Zamu Tarwatsa Cibiyoyin Makamashi Da Cibiyoyin Mai Din Iran Amurka
Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar Amurka
  • Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
  • Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
  • Kano: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Amince da Garo A Matsayin Mataimakinsa Na 2027 Afrika
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
  • Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
  • Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
  • An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.