Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika

Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran
Published: March 27, 2026 at 6:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Amurka Donlad Trump ya ce ‘yan kasar Iran, mutane ne da suka kware wajen tattaunawa kan cimma yarjejeniya, amma ya kara da cewa baya zaton zai yi wata yarjejeniya da su don kawo karshen yakin da Isra’ila da Amurka suke yi da Iran din.

Da yake magana yayin wata tattaunawa da majalisar ministoci a fadar White house, Trum yace yanzu Iran na da damar soke duk wani kudiri nasu na makamashin nukiliya har abada, su sauya manufa. Ya kara da cewa zamu ga idan suna so suyi hakan, idan kuma sun ki, zamu zame musu karfen kafa, mu ci gaba da aika musu da bama bamai.

Jawabin na Trump yayi biyo bayan matsin rayuwa da sanadin yakin ya jawo ke kara tsamari, inda ake fuskantar rashin isasshen man fetur da gas, abinda ya sa kamfanoni da kasashe tashi tsaye wajen kokarin shawo kan lamarin.

Jakadan Amurka na musamman, Steve Witkoff ya tabbatar da cewa Amurka ta aike da takarda mai dauke da ka’idoji 15, a matsayin hanyar da za’a bi don tattaunawa kan kawo karshen yakin, ya kara da cewa akwai alama cewa fadar gwamnatin Tehran nada sha’awar cimma yarjejeniya.

Ministan harkokin waje na kasar Pakistan yace tattaunawa tsakanin Amurka da iran na wanzuwa ne ta hanyar sakonni da ake aikowa ta hannun fadar gwamnatin Islamabad, tare da wasu kasashe da suka hada da Turkiyya da Masar, wanda suma suke goyon bayan tattaunawar sulhu.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta
Next Post: Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako

Karin Labarai Masu Alaka

Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai
Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
  • Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya Tsaro
  • Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai
  • Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.