Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
Published: April 17, 2026 at 7:51 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa da al’ummar Najeriya cewa gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen gina ƙasa mai dorewa, zaman lafiya, da wadata.

Shugaban ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar mambobin ƙungiyar Renewed Hope Ambassadors ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa tsarin siyasa da tattalin arziƙin da suka daɗe suna dakushe ci gaban ‘yan ƙasa, yanzu ana musanya su da sabbin tsare-tsare da za su ba kowa damar cin moriyar arziƙin ƙasa. Ya kuma sha alwashin ci gaba da aiwatar da garambawul ɗin da nufin samar wa talakawa da marasa ƙarfi guraben ayyukan yi da sauƙin rayuwa.

“Kuna wakiltar lamirin al’ummar da ke son kakkabe sarƙar talauci da yanke ƙauna,” in ji shugaban sa’ilin da yake jawabi ga tawagar.

Ya buƙaci ‘yan Najeriya kada su yarda da kalaman ɓata suna na ‘yan hamayya, inda ya ce idan ma ba su ganin ayyukan hanyoyi da gadoji da ake yi, to za a samar musu da gilashin gani don su gani da kyau.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da na jam’iyya, ciki har da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda, Gwamnoni da suka haɗa da na Yobe, Gombe, Kebbi, Ebonyi, Delta, Kogi, Ekiti, Benue, Taraba, Edo, da Kaduna, Tsofaffin Gwamnoni da Shugabannin Majalisa Kamar su Aminu Bello Masari, Ifeanyi Okowa, Tanko Al-Makura, da Anyim Pius Anyim.

A nasa jawabin, tsohon Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya yaba wa shugaban bisa ƙarfin halin aiwatar da sauye-sauyen da wasu shugabannin na baya suka kasa yi, musamman batun cire tallafin mai da haɗe farashin canjin kuɗi.

Masari ya tabbatar wa shugaban cewa jiga-jigan siyasar shiyyar Arewa maso Yamma suna bayansa ɗari bisa ɗari, kuma za su zagaya don duba ayyukan da gwamnatin tarayya ke yi a shiyyar domin wayar da kan jama’a.

Daga ƙarshe, Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin ƙungiyar da su ci gaba da isar da saƙon fatan alheri ga jama’a a matakin gundumomi da ƙauyuka, yana mai jaddada cewa “Najeriya tana hannun amintattu.”

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka
An Gargadi Kasar Canada Game Da Tura Sojoji Lebanon Afrika
Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika
Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika
  • Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
  • Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
  • Shirin Ga Fili GA Doki Shirye-Shirye
  • Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
  • Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
  • Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
  • ‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.