Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa
Published: December 20, 2025 at 12:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya ce ta lashe matsayi na ɗaya a rukunin maza a Gasar Karatun Al-Qur’ani ta Ƙasa ta shekarar 2025, wadda aka gudanar a Maiduguri ƙarƙashin taken “Borno 2025.”

Wannan gasa ta zama abin tarihi, domin ita ce karo na 40 da ake gudanarwa a Najeriya kuma Borno ta yi nasarar karɓar baƙuncinta cikin nasara.

Yayin sanar da sakamakon gasar, Daraktan Cibiyar Nazarin addinin Musulunci ta Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Abubakar Yelwa, ya bayyana Musa Ahmed Musa daga jihar Borno a matsayin zakaran a rukunin maza.

A rukunin mata kuma, Hafsat Muhammad Sada daga Jihar Kano ce ta zama Dawisu.

Gasar wadda ta ɗauki tsawon mako guda, ta samu mahalarta mutane 296 daga jihohi 30 na Najeriya, inda suka fafata a rukunai daban daban.

Da yake jawabi a bikin rufe gasar, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana nasarar gudanar da gasar a matsayin alamar dawowar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Borno.

Ya ce gasar ta nuna jajircewar al’ummar jihar wajen zaman lafiya, ilimi da koyarwar Musulunci.

“Nasarar ku ba kawai cin gasa ba ce,” in ji Gwamna Zulum ga waɗanda suka yi nasara, “amma wata babbar nasara ce da ta samo asali daga dogon lokaci na jajircewa, himma da girmama Kalmar Allah.”

Ya kuma yaba wa dukkan mahalarta gasar, inda ya ce, “Hakikanin ruhin wannan gasa ba wai lambobin yabo kawai ba ne, amma neman ilimi da jarumtar shiga gasar.”

Gwamnan ya nuna godiya ga Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, da matarsa Hajiya Nana Kashim Shettima, da sauran manyan baƙi da suka bayar da gudunmawa wajen samun nasarar gasar.

Haka kuma, ya yaba da rawar da sarakunan gargajiya, shugabannin jami’o’i, malaman addinai da shugabannin siyasa suka taka wajen nasarar taron.

Manyan baƙi da suka halarci taron sun haɗa da matar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Hajiya Nana Kashim Shettima, Gwamnan jihar Katsina, Alhaji Dikko Umar Radda, Mataimakin Gwamnan Jihar Sakkwato, Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ‘yan Majalisun Tarayya da jihohi da malaman addini.

Babban abin da ya kayatar a bikin shi ne rabon kyaututtuka da lambobin yabo ga waɗanda suka yi nasara, wanda matar Mataimakin Shugaban Ƙasa ta gabatar.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi
Next Post: Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika
Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika
Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
  • Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
  • Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai
  • Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
  • Rasha Na Cigaba Da Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Ga Ukrain Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.