Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai
Published: December 16, 2025 at 7:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Majalisar wakilan tarayyar Najeriya ta jefa kuri’ar amincewa da sanya baki wajen binciken rikicin da ya barke a tsakanin hukumar kula da jigila da tace danyen man fetur ta Najeriya da matatar mai ta Dangote, a sanadiyyar munakisar bayar da lasisin shiga da tataccen mai cikin kasar, da kuma kayyade farashinsa, yayin da ake zargin shugaban hukumar da wawurar makudan kudade.

Attajirin da ya fi kowa arzikin kudi a Najeriya, Aliko Dangote, ya zargi wannan hukuma da laifin bada lasisin shiga kasar da tataccen man fetur maras kyau da nufin gurgunta matatun tace man fetur na kasar, ciki har da mai tace ganga dubu 650 ta mai a kullum dake Lagos, wadda ita ce kuma mafi girma a duk fadin nahiyar Afirka.

Dangote ya bukaci da a gudanar da bincike akan shugaban hukumar Farouk Ahmed, wanda yayi zargi da rashin iya tafiyar da aiki, da kuma yadda ya kashe dubban miliyoyin Naira wajen tura ‘ya’yansa hudu karatun sakandare a kasar Switzerland, kudin da ba ya da wata hanyar da aka sani ta halal ta samu.

‘Yan majalisa sun yi kashedin cewa wannan rikici a tsakanin Dangote da hukumar yana iya haddasa karancin mai a daidai lokacin da ake tinkarar bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara, kuma tababa a kan hukumar kula da jigila da tace man na barazana ga tabbatar da samuwar makamashi da kashe kwarin guiwar masu zuba jari a fannin.

‘Yan majalisar suka ce matatar mai ta Dangote mai matukar muhimmanci ce ga tabbatar da tsaron makamashi a kasa wadda zata kawo karshen dogaron da Najeriya take yi a kan shigo da tataccen mai, da samarwa da kasar kudaden wajen da take matukar bukata, da ma sauko da farashin mai a cikin gida.

Ba a bayyana ranar da Kwamitin kula da harkokin man fetur na majalisar zai yi zama kan wannan batun ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA
Next Post: ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi

Karin Labarai Masu Alaka

Shari’ar Abubakar Malami Ta Kaura Zuwa Sabon Alkali Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
Ga Fili Ga Doki Najeriya
Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
  • Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
  • ‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
  • Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.