Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai
Published: December 16, 2025 at 7:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Majalisar wakilan tarayyar Najeriya ta jefa kuri’ar amincewa da sanya baki wajen binciken rikicin da ya barke a tsakanin hukumar kula da jigila da tace danyen man fetur ta Najeriya da matatar mai ta Dangote, a sanadiyyar munakisar bayar da lasisin shiga da tataccen mai cikin kasar, da kuma kayyade farashinsa, yayin da ake zargin shugaban hukumar da wawurar makudan kudade.

Attajirin da ya fi kowa arzikin kudi a Najeriya, Aliko Dangote, ya zargi wannan hukuma da laifin bada lasisin shiga kasar da tataccen man fetur maras kyau da nufin gurgunta matatun tace man fetur na kasar, ciki har da mai tace ganga dubu 650 ta mai a kullum dake Lagos, wadda ita ce kuma mafi girma a duk fadin nahiyar Afirka.

Dangote ya bukaci da a gudanar da bincike akan shugaban hukumar Farouk Ahmed, wanda yayi zargi da rashin iya tafiyar da aiki, da kuma yadda ya kashe dubban miliyoyin Naira wajen tura ‘ya’yansa hudu karatun sakandare a kasar Switzerland, kudin da ba ya da wata hanyar da aka sani ta halal ta samu.

‘Yan majalisa sun yi kashedin cewa wannan rikici a tsakanin Dangote da hukumar yana iya haddasa karancin mai a daidai lokacin da ake tinkarar bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara, kuma tababa a kan hukumar kula da jigila da tace man na barazana ga tabbatar da samuwar makamashi da kashe kwarin guiwar masu zuba jari a fannin.

‘Yan majalisar suka ce matatar mai ta Dangote mai matukar muhimmanci ce ga tabbatar da tsaron makamashi a kasa wadda zata kawo karshen dogaron da Najeriya take yi a kan shigo da tataccen mai, da samarwa da kasar kudaden wajen da take matukar bukata, da ma sauko da farashin mai a cikin gida.

Ba a bayyana ranar da Kwamitin kula da harkokin man fetur na majalisar zai yi zama kan wannan batun ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA
Next Post: ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa Najeriya
Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
  • Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro Labarai
  • Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
  • An Watse A Tattaunawar Tsakanin Rasha Da Ukraine Batare Da Cimma Matsaya Ba Labarai
  • Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.