Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai
Published: December 16, 2025 at 7:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Majalisar wakilan tarayyar Najeriya ta jefa kuri’ar amincewa da sanya baki wajen binciken rikicin da ya barke a tsakanin hukumar kula da jigila da tace danyen man fetur ta Najeriya da matatar mai ta Dangote, a sanadiyyar munakisar bayar da lasisin shiga da tataccen mai cikin kasar, da kuma kayyade farashinsa, yayin da ake zargin shugaban hukumar da wawurar makudan kudade.

Attajirin da ya fi kowa arzikin kudi a Najeriya, Aliko Dangote, ya zargi wannan hukuma da laifin bada lasisin shiga kasar da tataccen man fetur maras kyau da nufin gurgunta matatun tace man fetur na kasar, ciki har da mai tace ganga dubu 650 ta mai a kullum dake Lagos, wadda ita ce kuma mafi girma a duk fadin nahiyar Afirka.

Dangote ya bukaci da a gudanar da bincike akan shugaban hukumar Farouk Ahmed, wanda yayi zargi da rashin iya tafiyar da aiki, da kuma yadda ya kashe dubban miliyoyin Naira wajen tura ‘ya’yansa hudu karatun sakandare a kasar Switzerland, kudin da ba ya da wata hanyar da aka sani ta halal ta samu.

‘Yan majalisa sun yi kashedin cewa wannan rikici a tsakanin Dangote da hukumar yana iya haddasa karancin mai a daidai lokacin da ake tinkarar bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara, kuma tababa a kan hukumar kula da jigila da tace man na barazana ga tabbatar da samuwar makamashi da kashe kwarin guiwar masu zuba jari a fannin.

‘Yan majalisar suka ce matatar mai ta Dangote mai matukar muhimmanci ce ga tabbatar da tsaron makamashi a kasa wadda zata kawo karshen dogaron da Najeriya take yi a kan shigo da tataccen mai, da samarwa da kasar kudaden wajen da take matukar bukata, da ma sauko da farashin mai a cikin gida.

Ba a bayyana ranar da Kwamitin kula da harkokin man fetur na majalisar zai yi zama kan wannan batun ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA
Next Post: ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Amince Da Gyaran Fadar Sarkin Gombe Afrika
Jami’an Tsaro Sun Dakile Safarar Makamai Daga Jos Zuwa Jihar Neja Afrika
Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika
Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha: Tura Sojojin Birtaniya Ukraine Zai Kara Ta’azzara Yaki Labarai
  • Yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 Najeriya
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya Afrika
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.