Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa
Published: February 27, 2026 at 4:43 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Akwai manyan batutuwa ko rashin fahimta dake kunno kai a yarjejeniyar kiwon lafiya da Amurka take kullawa da kasashen Afirka dangane da yadda tallafin kudi da Amurka take bayarwa zai rika aiki daga yanzu, kamar yadda shugaban hukumar sa ido da hana yaduwar cututtuka a Afirka ya fada ranar Alhamis.

“Akwai damuwa sosai game da musayar bayanai dana cututtuka, inji darekta janar na hukumar Jean Kesaya ya fadawa taron manema labarai ta hanyoyin sadarwa na zamani.

Ranar Laraba, Zimbabwe ta janye daga shawarwari da Amurka kan tallafin kudi dala milyan 367 cikin shekaru biyar masu zuwa, ta nuna damuwa kan musayar muhimman bayanai, tana mai cewa yarjejeniyar babu adalci. Zambia ma tace ta nuna rashin gamsuwarta da tsarin.

Wasu masu raji kan kiwon lafiya sun soki tsari da ya bukaci kasashe ba-da-wani-bata-lokaci ba, su sanarda Washington idan aka sami bullar wata cuta mai yaduwa a zaman sharadin bada tallafin. Yarjejeniyoyin basu bada tabbacin idan aka hada maganin da zai shawo kan cuta ko cututtukan za’a raba da kasashen da cutuutkan suka bullo ba.

Ahalinda ake ciki kuma, a cikin wata sanarwa ta hadin guiwa da Amurka da jamhuriyar demokuradiyyar kwango suka sanyawa hanu ranar Alhamis, ta nuna kasashen biyu sun amince da yarjejeniyar aiki ta fuskar kiwon lafiya kan kudi dala bilyan daya da milyan dari biyu, cikin shekaru biyar masu zuwa.

Yarjejeniyar zata maida hankali kan yaki da cutar dake karya garkuwar jiki, da ake yi wa lakabin HIV/AIDS da turanci, da cutar Malaria, da kuma kula da lafiyar iyaye mata masu juna biyu da jarirai, yaki da cutar shan inno ko polio, da kuma sa ido kan pullar cututtuka masu yaduwa, kamar yadda sanarwar ta fada.

Afrika, Amurka, Kimiya, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC
Next Post: Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar Afrika
Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira Amurka
Wasu Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Kwango Afrika
Hamas Ta Kwance Damara Afrika
Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
  • Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Ana Kokarin Dawo Da Wutan Lantarki A Cuba Afrika
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
  • Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.