Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa
Published: February 27, 2026 at 4:43 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Akwai manyan batutuwa ko rashin fahimta dake kunno kai a yarjejeniyar kiwon lafiya da Amurka take kullawa da kasashen Afirka dangane da yadda tallafin kudi da Amurka take bayarwa zai rika aiki daga yanzu, kamar yadda shugaban hukumar sa ido da hana yaduwar cututtuka a Afirka ya fada ranar Alhamis.

“Akwai damuwa sosai game da musayar bayanai dana cututtuka, inji darekta janar na hukumar Jean Kesaya ya fadawa taron manema labarai ta hanyoyin sadarwa na zamani.

Ranar Laraba, Zimbabwe ta janye daga shawarwari da Amurka kan tallafin kudi dala milyan 367 cikin shekaru biyar masu zuwa, ta nuna damuwa kan musayar muhimman bayanai, tana mai cewa yarjejeniyar babu adalci. Zambia ma tace ta nuna rashin gamsuwarta da tsarin.

Wasu masu raji kan kiwon lafiya sun soki tsari da ya bukaci kasashe ba-da-wani-bata-lokaci ba, su sanarda Washington idan aka sami bullar wata cuta mai yaduwa a zaman sharadin bada tallafin. Yarjejeniyoyin basu bada tabbacin idan aka hada maganin da zai shawo kan cuta ko cututtukan za’a raba da kasashen da cutuutkan suka bullo ba.

Ahalinda ake ciki kuma, a cikin wata sanarwa ta hadin guiwa da Amurka da jamhuriyar demokuradiyyar kwango suka sanyawa hanu ranar Alhamis, ta nuna kasashen biyu sun amince da yarjejeniyar aiki ta fuskar kiwon lafiya kan kudi dala bilyan daya da milyan dari biyu, cikin shekaru biyar masu zuwa.

Yarjejeniyar zata maida hankali kan yaki da cutar dake karya garkuwar jiki, da ake yi wa lakabin HIV/AIDS da turanci, da cutar Malaria, da kuma kula da lafiyar iyaye mata masu juna biyu da jarirai, yaki da cutar shan inno ko polio, da kuma sa ido kan pullar cututtuka masu yaduwa, kamar yadda sanarwar ta fada.

Afrika, Amurka, Kimiya, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC
Next Post: Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Kasashe 5 Da Ke Fama Da Matsanancin Zazzabin Cizon Sauro Rediyo
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
  • Tsarin Haraji Mai Cike Da Ayoyin Tambaya Na Shirin Fara Aiki Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.