Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika

Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa
Published: February 12, 2026 at 8:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe ta ce ta samu nasarar ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a kauyen Tingile, yankin Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada a jihar Gombe Najeriya.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe uku na daren ranar 11 ga Fabrairu, 2026, lokacin da wasu mutane da ba a san ko su waye ba, dauke da sanduna, adduna da wukake, suka kai hari rumfar kiwon shanun Alhaji Adamu Bappah mai shekaru 48.

Sanarwar ta ce maharan sun doke shi tare da dansa, inda dan ya samu raunuka, kafin daga bisani su yi awon gaba da Alhaji Adamu zuwa wani wuri da ba a sani ba. An garzaya da dansa asibiti domin kula da lafiyarsa.

Sai dai rundunar ta ce cikin gaggawa jami’anta, tare da hadin gwiwar mafarauta da ’yan sa-kai, suka kaddamar da samame a wannan rana da misalin karfe uku na rana. Hakan ya kai ga ceto mutumin a dajin Dawo da ke Karamar Hukumar Kwami.

Bayan ceto shi, an kai shi asibiti domin a duba lafiyarsa kafin daga bisani ya koma hannun iyalansa lafiya.

Rundunar ta kara da cewa ana ci gaba da kokarin cafke wadanda ake zargi da aikata laifin, domin su fuskanci hukunci.

’Yan sandan sun sake jaddada kudurinsu na tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin jihar Gombe.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv
Next Post: Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya

Karin Labarai Masu Alaka

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha: Tura Sojojin Birtaniya Ukraine Zai Kara Ta’azzara Yaki Labarai
Shugaban Kasar Ukraine Yace Rasha Tana Bawa Iran Bayanan Sirri Afrika
Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa Afrika
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
  • Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
  • Farashin Mai Ya Ragu A Kasuwar Duniya Amurka
  • Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
  • Addini Ko Kabilanci Basu Da Gurbi Cikin Ta’addanci Labarai
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.