Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa
Published: February 12, 2026 at 8:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe ta ce ta samu nasarar ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a kauyen Tingile, yankin Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada a jihar Gombe Najeriya.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe uku na daren ranar 11 ga Fabrairu, 2026, lokacin da wasu mutane da ba a san ko su waye ba, dauke da sanduna, adduna da wukake, suka kai hari rumfar kiwon shanun Alhaji Adamu Bappah mai shekaru 48.

Sanarwar ta ce maharan sun doke shi tare da dansa, inda dan ya samu raunuka, kafin daga bisani su yi awon gaba da Alhaji Adamu zuwa wani wuri da ba a sani ba. An garzaya da dansa asibiti domin kula da lafiyarsa.

Sai dai rundunar ta ce cikin gaggawa jami’anta, tare da hadin gwiwar mafarauta da ’yan sa-kai, suka kaddamar da samame a wannan rana da misalin karfe uku na rana. Hakan ya kai ga ceto mutumin a dajin Dawo da ke Karamar Hukumar Kwami.

Bayan ceto shi, an kai shi asibiti domin a duba lafiyarsa kafin daga bisani ya koma hannun iyalansa lafiya.

Rundunar ta kara da cewa ana ci gaba da kokarin cafke wadanda ake zargi da aikata laifin, domin su fuskanci hukunci.

’Yan sandan sun sake jaddada kudurinsu na tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin jihar Gombe.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv
Next Post: Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS Afrika
Jam’iyyar APC Ta Ayana Jamilu Gwamna A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Gombe Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Daƙile Yaɗuwar Makamai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Afrika
Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
  • Wakilan Rasha Da Ukraine Sun Tattauna A Abu Dhabi Ranar Juma’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC Siyasa
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.