Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos
Published: April 2, 2026 at 1:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, a ranar Alhamis 2 ga Afrilu, 2026, ya jagoranci shugabannin hukumomin tsaro domin duba halin tsaro kai tsaye a birnin Jos na jihar Filato

Mukaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Soji, Kanal Appolonia Anele, ta bayyana a wata sanarwa cewa ziyarar na daga cikin ƙoƙarin dawo da zaman lafiya da tabbatar da dorewar sa a faɗin jihar.

Sanarwar ta ce, bayan isowarsa ya samu tarba daga gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, a matsayin alamar kyakkyawar haɗin gwiwa tsakanin farar hula da sojoji wajen magance matsalolin tsaro.

Haka kuma, COAS ya karɓi cikakken bayani kan ayyukan tsaro daga Babban Kwamandan Runduna ta 3 da kuma Kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta Operation ENDURING PEACE, Manjo Janar Folusho Oyinlola, wanda ya yi bayani kan matakan da ake ɗauka tare da sauran hukumomin tsaro domin dakile barazana, kare rayuka da dukiyoyi, da kuma daidaita al’ummomin da abin ya shafa.

A yayin ziyarar, Laftanar Janar Waidi Shaibu ya gana da shugabannin al’umma da mazauna yankin, inda ya tabbatar musu da ƙudirin rundunar sojin kasa ta Najeriya na kare rayukan dukkan ‘yan ƙasa masu bin doka.

Ya kuma buƙaci al’umma su kasance cikin natsuwa da taka-tsantsan, su kuma mara wa hukumomin tsaro baya ta hanyar bin dokar takaita zirga-zirga (curfew) da kuma ba da cikakken haɗin kai a ayyukan bincike da tsaro, yayin da suke gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Shugaban ƙaramar hukumar Jos ta Arewa, Mr. Dachung Bagos, ya yaba da ziyarar COAS, yana mai cewa zuwan manyan shugabannin soji zai ƙara wa jama’a kwarin gwiwa tare da ƙarfafa amincewa da matakan tsaro da ake ɗauka.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi
Next Post: Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan

Karin Labarai Masu Alaka

Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
Kasar Jamus Ta Haramtawa Yara Kasa Da Shekaru 14 Hawa Dandalin Sada Zumunta Labarai
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Duniyar Dambe A Makon Jiya Nishadi
  • Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
  • Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika
  • Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
  • Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika
  • Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya
  • Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.