Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki
Published: June 22, 2026 at 12:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mataimakin Sufeto Janar na ’Yan Sanda (DIG) mai kula da shiyar Arewa Maso Gabas, Zakariyya Fera, da Ibrahim Baba Zango sun buƙaci masu ruwa da tsaki da su ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da hukumomin tsaro domin daƙile ayyukan masu aikata laifuka da magance matsalolin tsaro a yankin.

DIG Fera da Baba Zango sun bayyana hakan ne a yayin taron tuntuba da masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Hedikwatar Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe.

A jawabinsa na maraba, Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya ce rundunar na ci gaba da ba da fifiko ga aikin ’yan sanda na kusanci da al’umma da kuma inganta tsaro ta hanyar haɗin gwiwa da jama’a.

Da yake jawabi a taron, DIG Fera ya ce manufar ziyararsa ita ce neman haɗin kai da goyon bayan masu ruwa da tsaki wajen yaƙi da masu aikata laifuka. Ya jaddada cewa rundunar ’yan sanda ba za ta iya cimma nasara a aikinta ba tare da sahihan bayanan sirri, haɗin kan al’umma da musayar ra’ayoyi masu amfani daga jama’a.

Ya bayyana cewa tsarin gudanar da aikin ’yan sanda ya kan bambanta daga jiha zuwa jiha, gwargwadon irin ƙalubalen tsaron da ake fuskanta a kowace jiha. Ya kuma ce Sufeto Janar na ’Yan Sanda na ci gaba da ƙarfafa tsarin aikin tsaro da ya ginu kan haɗin kai da jama’a.

DIG ɗin ya yi gargaɗi kan take haƙƙin ɗan Adam, rashin ɗa’a daga wasu jami’an tsaro, rikice-rikicen tsakanin al’umma da sauran ayyukan da ka iya kawo barazana ga zaman lafiya. Ya tabbatar da cewa rundunar tana da manufar rashin lamuntar duk wani nau’i na cin zarafi, rashin ɗa’a ko karya doka daga jami’anta.

Ya ƙara da cewa Sufeto Janar na ’Yan Sanda na neman cikakken goyon bayan jama’a domin cimma manufofin rundunar, musamman wajen hana aikata laifuka da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

A jawabinsa Sakataren Gwamnatin jihar Gombe, Wanda yasamu wakilincin Alhaji Salihu Adamu Sambo, Babban Sakatare a Ofishin Sakataren Gwamnatin jihar ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar wajen tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Ya ce babu wani ci gaba mai ma’ana da za a samu ba tare da zaman lafiya da tsaro ba, yana mai tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken goyon baya.

Ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar ta kafa Gombe State Security, Traffic and Environmental Corps (GOSTEC) domin haɗa kai da sauran hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Hakazalika, ya yi kira ga al’umma da su taka muhimmiyar rawa wajen magance tushen matsalolin rashin tsaro ta hanyar haɗin kai, sa ido da kuma bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.

A nasu jawaban, Sakataren Jama’atu Nasril Islam, Malam Saleh Danburam, Shugaban Kwamitin Hulɗa Tsakanin ’Yan Sanda da Al’umma (PCRC), Kwamared Garba Ubale, da Shugaban Ƙungiyoyin Farar Hula, Ibrahim “3000”, sun yaba da kyakkyawar alaƙa da haɗin gwiwar da ke tsakanin hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki a jihar.

Sun kuma yi alƙawarin ci gaba da bai wa jami’an tsaro cikakken haɗin kai da goyon baya, tare da yabawa kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya da al’ummar Jihar Gombe, musamman ƙarƙashin jagorancin CP Umar Ahmed Chuso.

Masu jawabin sun yaba da saurin kai ɗauki da rundunar ’yan sandan jihar ke yi a lokutan gaggawa, tare da kira gare ta da ta ci gaba da wannan kyakkyawan aiki domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe
Next Post: Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas

Karin Labarai Masu Alaka

Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika
Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai
Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • Tashoshin Mai Basa Iya Loda Mai A Rasha Labarai
  • Shugaban Amurka Ya Sauke Antoni Janar Amurka
  • Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
  • Gwamnatin Amurka Tana Ganawa Da Manyan Jami’an Leken Asiri Amurka
  • Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu Najeriya
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.