Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano
Published: January 14, 2026 at 8:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da asibitocin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar wata matar aure mai suna Aishatu Umar, wadda ake zargin ta rasu sakamakon sakaci a aikin likitanci bayan an yi mata tiyata a asibitin Abubakar Imam.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar, Samira Suleiman, ta fitar a ranar Talata.

“Kwamitin Kula da Asibitocin jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Babban Sakatare, Dakta Mansur Mudi Nagoda, ya lura da rahoton da ya tayar da hankula game da rasuwar Aishatu Umar.

“Muna miƙa ta’aziyyarmu ga iyalanta da masoyanta. Babban Sakatare ya bayar da umarnin a gaggauta gudanar da cikakken bincike kan zargin da aka yi a asibitin Abubakar Imam domin gano gaskiya da abin da ya faru,” in ji ta.

Hukumar ta tabbatar wa jama’a cewa binciken zai kasance a bayyane, ba tare da son zuciya ba, kuma cikin ƙwarewa, tare da ƙara da cewa za a ɗauki matakan da suka dace bisa ƙa’idoji idan aka tabbatar da wani sakaci.

Idan za iya tunawa cewa an rawaito marigayiya Aishatu Umar ta rasu ne bayan abin da iyalanta suka bayyana a matsayin zargin sakaci a aikin likitanci bayan an yi mata tiyata a asibitin.

A cewar wani ɗan uwanta, Mohammed, wanda ya wallafa a shafin Facebook, marigayiya Aishatu, matar aure mai ‘ya’ya biyar, ta rasu da misalin ƙarfe 1 na dare a ranar Talata bayan ta sha fama da ciwon ciki mai tsanani tun bayan tiyatar da aka yi mata a watan Satumba na 2025.

“Ta fara korafin ciwon ciki mai tsanani wanda ya ci gaba har tsawon watanni. Ta sha wannan ciwo na tsawon watanni huɗu,” in ji Mohammed.

Ya yi zargin cewa duk da yawan komawarta asibitin, ma’aikatan lafiya suna ba ta magungunan rage zafi ne kawai su sallame ta ba tare da yin cikakken bincike ba.

Mohammed ya ƙara da cewa sai kwanaki biyu kacal kafin rasuwarta ne aka yi mata cikakkun gwaje-gwaje da hotunan bincike (scanning), waɗanda suka nuna wai an bar almakashi guda biyu a cikin jikinta tun lokacin tiyatar watan Satumba.

“An fara shirye-shiryen yin gyaran tiyata, amma lokacin nata ya ƙare,” in ji shi.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka
Next Post: Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu

Karin Labarai Masu Alaka

Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi A Edo Afrika
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojoji Zasu Taimakawa ‘Yan Sanda Wajen Yaki Da Mugayen Ayyuka Labarai
  • Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
  • Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
  • Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
  • ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji Najeriya
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.