Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar
Published: February 28, 2026 at 3:53 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa an sace yara 48 ‘yan asalin jihar masu shekaru tsakanin biyu zuwa biyar, inda ya ce an kai su wasu sassan duniya kamar yadda jaridar The Cable ta rawaito.

Inuwa Yahaya ya yi wannan bayani ne yayin ƙaddamar da rabon tallafin Abincin Ramadan a Gombe, inda ya nuna damuwa kan rashin tabbacin ko za a sake samun yaran lafiya.

Yace tsaro alhakin kowa ne, tare da buƙatar mazauna jihar su mara wa matakan gwamnati baya domin dakile barazanar da ke addabar zaman lafiya.

Gwamnan ya kuma ce dokar hana cinikin ƙarafa da takaita amfani da babura an ɗauke su ne domin inganta tsaro da rage satar ababen hawa.

Haka zalika, ya koka kan lalata kayayyakin more rayuwa, inda ya ce an taɓa kayayyakin wutar lantarki na Muhammadu Buhari Industrial Park da kuma madatsar ruwa ta Dadin Kowa Dam.

Ya ƙara da cewa mutane 70,000 ne za su amfana da tallafin Ramadan, tare da umartar kwamitin rabon kayayyakin da su tabbatar da gaskiya da adalci kuma Suyi rabon a cikin mako daya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu
Next Post: Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Barayin Waya Sun Yanke Yatsun Hannu Guda Biyu Da Gefen Kunne A Bauchi Labarai
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi A Edo Afrika
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
  • Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
  • An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.