Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar
Published: February 28, 2026 at 3:53 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa an sace yara 48 ‘yan asalin jihar masu shekaru tsakanin biyu zuwa biyar, inda ya ce an kai su wasu sassan duniya kamar yadda jaridar The Cable ta rawaito.

Inuwa Yahaya ya yi wannan bayani ne yayin ƙaddamar da rabon tallafin Abincin Ramadan a Gombe, inda ya nuna damuwa kan rashin tabbacin ko za a sake samun yaran lafiya.

Yace tsaro alhakin kowa ne, tare da buƙatar mazauna jihar su mara wa matakan gwamnati baya domin dakile barazanar da ke addabar zaman lafiya.

Gwamnan ya kuma ce dokar hana cinikin ƙarafa da takaita amfani da babura an ɗauke su ne domin inganta tsaro da rage satar ababen hawa.

Haka zalika, ya koka kan lalata kayayyakin more rayuwa, inda ya ce an taɓa kayayyakin wutar lantarki na Muhammadu Buhari Industrial Park da kuma madatsar ruwa ta Dadin Kowa Dam.

Ya ƙara da cewa mutane 70,000 ne za su amfana da tallafin Ramadan, tare da umartar kwamitin rabon kayayyakin da su tabbatar da gaskiya da adalci kuma Suyi rabon a cikin mako daya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu
Next Post: Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta

Karin Labarai Masu Alaka

APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Ya Hallaka Mutane Uku A Jihar Yobe Labarai
Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz Amurka
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
  • Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
  • Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF Wasanni
  • Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar Afrika
  • Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.