Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar
Published: February 28, 2026 at 3:53 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa an sace yara 48 ‘yan asalin jihar masu shekaru tsakanin biyu zuwa biyar, inda ya ce an kai su wasu sassan duniya kamar yadda jaridar The Cable ta rawaito.

Inuwa Yahaya ya yi wannan bayani ne yayin ƙaddamar da rabon tallafin Abincin Ramadan a Gombe, inda ya nuna damuwa kan rashin tabbacin ko za a sake samun yaran lafiya.

Yace tsaro alhakin kowa ne, tare da buƙatar mazauna jihar su mara wa matakan gwamnati baya domin dakile barazanar da ke addabar zaman lafiya.

Gwamnan ya kuma ce dokar hana cinikin ƙarafa da takaita amfani da babura an ɗauke su ne domin inganta tsaro da rage satar ababen hawa.

Haka zalika, ya koka kan lalata kayayyakin more rayuwa, inda ya ce an taɓa kayayyakin wutar lantarki na Muhammadu Buhari Industrial Park da kuma madatsar ruwa ta Dadin Kowa Dam.

Ya ƙara da cewa mutane 70,000 ne za su amfana da tallafin Ramadan, tare da umartar kwamitin rabon kayayyakin da su tabbatar da gaskiya da adalci kuma Suyi rabon a cikin mako daya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu
Next Post: Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta

Karin Labarai Masu Alaka

An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai
Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
Azumin Ramadan Yahadu Da Azumin Lent Da Mabiya Addinin Kirista Sukeyi A Wannan Shekarar Labarai
Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
  • Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
  • Hawan Sallah Daga Masarautar Misau Afrika
  • Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
  • Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
  • Yusuf Gawuna Ya Koma Jam’iyar ADC Afrika
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
  • Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.