Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa
Published: February 9, 2026 at 9:34 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Hukumar Alhazai Alhaji Abdullahi Saleh Pakistan, ya sanar da sauka daga mukaminsa. An bayyana cewa ya yanke wannan shawara ne bayan nazari da tuntuba, domin bai wa wasu damar ci gaba da jagoranci tare da kawo sabbin dabaru a aikin hukumar.

A cikin sanarwar da ya fitar, Alhaji Abdullahi Saleh Pakistan ya gode wa ma’aikata, shugabanni da al’ummar da suka ba shi goyon baya a tsawon lokacin da ya rike mukamin, inda ya jaddada cewa hukumar ta samu nasarori da dama a karkashinsa.

Haka kuma, ya bukaci dukkan masu ruwa da tsaki da su ci gaba da bai wa hukumar hadin kai domin inganta ayyukan da suka shafi alhazai da walwalar al’umma gaba ɗaya.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a sanar da wanda zai gaje shi a hukumance ba, sai dai ana sa ran hukumomin da abin ya shafa za su fitar da karin bayani nan gaba.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari
Next Post: Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Birai Afrika
Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
  • Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
  • Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
  • Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka
  • An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
  • Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25 Shirye-Shirye
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.