Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari
Published: February 9, 2026 at 8:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan sadarwan kasar Uganda, Chris Baryomunsi ya yi Allah wadai da samamen da sojoji suka kai gidan dan jam’iyyar adawa Bobi Wine a watan da ya wuce. Ya kuma shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa, Wine be aikata wani lefi ba, kuma yana da damar dawowa gidan sa.

Baryomunsi, wanda kuma shine mai magana da yawun gwamnati ya ce hukumomi zasu yi bincike kan lamarin.

Wine ya shafe makonni a boye, bayan da ya tsere daga gidan sa dake Kampala babban birnin kasar, awanni kafin sanar da shi ne ya zo na biyu a sakamakon zaben da aka gudanar ranar 15 ga watan Janairu, inda shugaba Yoweri Museveni ya yi nasarar lashewa.

Ranar 24 ga Watan Janairu ne, Wine ya ce sojoji sun afka gidan sa, har suka ji ma matar sa ciwo. Shugaban sojojin Uganda Muhoozi Kainerugaba, wanda da ne ga Yoweri Museveni ya musanta zargin cin zarafin matar Wine.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro
Next Post: Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa

Karin Labarai Masu Alaka

Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya
  • 2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Farashin Zinari Yayi Tashin Gwauron Zabi Amurka
  • An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.