A birnin Mineapolis na jihar Minnesta, mutumin da jami’an shige da fice na Amurka suka harba ranar Asabar, ya mutu, kamar yadda jami’an jihar dana tarayya suka fada, wanda shine mutum na biyu da jami’an tarayya suka harba suka kashe a birnin dake arewacin kasar.
Mutumin wanda ba’a bayyana ko wanene ba, hukumar kula da harkokin cikin gida na Amurka tace yana da bindiga da kurtun albarusai biyu.
Wani video da ake yadawa a kafofin sada zumunta, kuma wasu tashoshin talabijin suka nuna, anga mutane da suka rufe fuskokinsu sanye da sulke, suna kokawa da wani mutum a wani titi da kankara, sai kuma aka ji karan bindiga, a videon, anga mutumin ya fadi kasa, sanan aka ji karin harbe harbe.
Gwamnan jihar Minnesota, Tim Waltz yayi kira da a kawo karshen matakin gwamnatin Trump na yaki da bakin haure a jihar ba tare da wani bata lokaci ba. A sako da ya wallafa a shafinsa na X, Gwamna Tim Waltz yace yayi magana da fadar White House bayan wani mummunar harbi mai tada hankali da jami’an gwamnatin tarayya suka yi da safiyar ranar asabar. Tilas shugaban kasa ya kawo karshen wannan aiki.
Jami’ai a matakin karamar hukuma a yankin, a wani sako da suka wallafa a kafofin sada zumunta, sun kira yi jama’a su kai zuciya nesa, kuma kauracewa inda al’amarin yafaru.


