Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira
Published: January 24, 2026 at 8:30 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A birnin Mineapolis na jihar Minnesta, mutumin da jami’an shige da fice na Amurka suka harba ranar Asabar, ya mutu, kamar yadda jami’an jihar dana tarayya suka fada, wanda shine mutum na biyu da jami’an tarayya suka harba suka kashe a birnin dake arewacin kasar.

Mutumin wanda ba’a bayyana ko wanene ba, hukumar kula da harkokin cikin gida na Amurka tace yana da bindiga da kurtun albarusai biyu.

Wani video da ake yadawa a kafofin sada zumunta, kuma wasu tashoshin talabijin suka nuna, anga mutane da suka rufe fuskokinsu sanye da sulke, suna kokawa da wani mutum a wani titi da kankara, sai kuma aka ji karan bindiga, a videon, anga mutumin ya fadi kasa, sanan aka ji karin harbe harbe.

Gwamnan jihar Minnesota, Tim Waltz yayi kira da a kawo karshen matakin gwamnatin Trump na yaki da bakin haure a jihar ba tare da wani bata lokaci ba. A sako da ya wallafa a shafinsa na X, Gwamna Tim Waltz yace yayi magana da fadar White House bayan wani mummunar harbi mai tada hankali da jami’an gwamnatin tarayya suka yi da safiyar ranar asabar. Tilas shugaban kasa ya kawo karshen wannan aiki.

Jami’ai a matakin karamar hukuma a yankin, a wani sako da suka wallafa a kafofin sada zumunta, sun kira yi jama’a su kai zuciya nesa, kuma kauracewa inda al’amarin yafaru.

Amurka

Post navigation

Previous Post: An Watse A Tattaunawar Tsakanin Rasha Da Ukraine Batare Da Cimma Matsaya Ba
Next Post: Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi

Karin Labarai Masu Alaka

Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
  • Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.