Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya
Published: February 13, 2026 at 5:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 13, 2026

Za Iya Juyin Juya Hali A Najeriya In A Ka Cigaba Da Take Hakkin Dan’adam -Inji Atiku Abubakar Kan Yunkurin Kama Elrufai

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya yi gargadin za a iya samun juyin jiuya hali matukar a ka cigaba da take hakkin jama’a na Dan’adam.

Alhaji Atiku Abubakar na magana ne a ziyarar jaje da ya kai wa tsohon gwamnan Kaduna Nasiru Elrufai wanda jami’an hukumar Efcc su ka yi yunkurin kama shi bayan dawowa daga tafiya a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe a Abuja.

“Ka rike manyan mukamai a kasar nan, ka yi minister, ka yi gwamna kuma ka sauke nauyin da ka ke kanka. Ba bukatar zubar ma ka da mutunci, domin zubar ma ka mutunci tamkar zubar da mutuncin dukkan ajin ‘yan siyasa ne” Inji Atiku Abubakar.

A nan Atiku wanda jigo ne a sabuwar jam’iyyar hadaka ta ADC da Elrufai ke ciki, ya yi gargadin irin wannan yunkuri da ya zayyana da take hakkin Dan’adam ke iya haddasa juyin juya hali.

Kamar sun hada baki da Elrufai kan batun jiran Elrufa’in ya dawo gida gabanin daukar wani mataki ta hanyar mika ma sa takardar gayyata a hukumance maimakon yunkurin cafke shi kenan ta wannan hanyar aiki da cikawa.

Jama’a dai tun farko sun yi dafifi su ka hana jami’an Efcc yunkurin kama Elrufai cewa hakan ba zai yiwu ba sai an bi ta hanyar da su ke ganin ta dace.

Tsohon gwamnan ya yi wata magana da wasu ke ganin ta wuce yanayin wani dan kasa gama-gari ya iya fada ya kwana lafiya yayin da ya shaidawa jami’an Efcc ko shugaban kasa ba zai fada ma sa abun da zai yi ba “ko shugaban kasa ba zai fada mi ni abunda zan yi ba

Hukumomi dai sun amshe fasfo din Elrufai kuma da alamu zai amsa gayyatar Efcc a tsanake.

Hukuamr ta yaki da cin hanci ta sha nanata ba ta daukar mataki kan wani haka kawai sai ta samu hujjoji kwarara.

Kakakin hukumar Dele Oyewole na cewa Efcc na hukunta mutane kan laifinsu ba don wata wariya ko tsana ba.

In za a tuna shi ma tsohon ministan shari’a Abubakar Malami ya samu kansa a wannan dambarwa bayan samun beli daga kotu amma jami’an DSS su ka sake awun gaba da shi.

Ga Rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya Daga Abuja

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/AUD-20260213-WA0000.mp3
Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu
Next Post: Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba

Karin Labarai Masu Alaka

An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika
Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC Siyasa
3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
  • Sojoji Sunkai Farmaki Gidan Dan Adawa A Kasar Uganda Bobi Wine Afrika
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland Amurka
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau Labarai
  • An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.