Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya
Published: February 13, 2026 at 5:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 13, 2026

Za Iya Juyin Juya Hali A Najeriya In A Ka Cigaba Da Take Hakkin Dan’adam -Inji Atiku Abubakar Kan Yunkurin Kama Elrufai

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya yi gargadin za a iya samun juyin jiuya hali matukar a ka cigaba da take hakkin jama’a na Dan’adam.

Alhaji Atiku Abubakar na magana ne a ziyarar jaje da ya kai wa tsohon gwamnan Kaduna Nasiru Elrufai wanda jami’an hukumar Efcc su ka yi yunkurin kama shi bayan dawowa daga tafiya a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe a Abuja.

“Ka rike manyan mukamai a kasar nan, ka yi minister, ka yi gwamna kuma ka sauke nauyin da ka ke kanka. Ba bukatar zubar ma ka da mutunci, domin zubar ma ka mutunci tamkar zubar da mutuncin dukkan ajin ‘yan siyasa ne” Inji Atiku Abubakar.

A nan Atiku wanda jigo ne a sabuwar jam’iyyar hadaka ta ADC da Elrufai ke ciki, ya yi gargadin irin wannan yunkuri da ya zayyana da take hakkin Dan’adam ke iya haddasa juyin juya hali.

Kamar sun hada baki da Elrufai kan batun jiran Elrufa’in ya dawo gida gabanin daukar wani mataki ta hanyar mika ma sa takardar gayyata a hukumance maimakon yunkurin cafke shi kenan ta wannan hanyar aiki da cikawa.

Jama’a dai tun farko sun yi dafifi su ka hana jami’an Efcc yunkurin kama Elrufai cewa hakan ba zai yiwu ba sai an bi ta hanyar da su ke ganin ta dace.

Tsohon gwamnan ya yi wata magana da wasu ke ganin ta wuce yanayin wani dan kasa gama-gari ya iya fada ya kwana lafiya yayin da ya shaidawa jami’an Efcc ko shugaban kasa ba zai fada ma sa abun da zai yi ba “ko shugaban kasa ba zai fada mi ni abunda zan yi ba

Hukumomi dai sun amshe fasfo din Elrufai kuma da alamu zai amsa gayyatar Efcc a tsanake.

Hukuamr ta yaki da cin hanci ta sha nanata ba ta daukar mataki kan wani haka kawai sai ta samu hujjoji kwarara.

Kakakin hukumar Dele Oyewole na cewa Efcc na hukunta mutane kan laifinsu ba don wata wariya ko tsana ba.

In za a tuna shi ma tsohon ministan shari’a Abubakar Malami ya samu kansa a wannan dambarwa bayan samun beli daga kotu amma jami’an DSS su ka sake awun gaba da shi.

Ga Rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya Daga Abuja

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/AUD-20260213-WA0000.mp3
Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu
Next Post: Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba

Karin Labarai Masu Alaka

Rangadin Ayyukan Tinubu Ya Kai Tawaga Zuwa Kano Northern Bypass Afrika
Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan Labarai
  • Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
  • Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
  • Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.