Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya
Published: February 13, 2026 at 5:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 13, 2026

Za Iya Juyin Juya Hali A Najeriya In A Ka Cigaba Da Take Hakkin Dan’adam -Inji Atiku Abubakar Kan Yunkurin Kama Elrufai

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya yi gargadin za a iya samun juyin jiuya hali matukar a ka cigaba da take hakkin jama’a na Dan’adam.

Alhaji Atiku Abubakar na magana ne a ziyarar jaje da ya kai wa tsohon gwamnan Kaduna Nasiru Elrufai wanda jami’an hukumar Efcc su ka yi yunkurin kama shi bayan dawowa daga tafiya a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe a Abuja.

“Ka rike manyan mukamai a kasar nan, ka yi minister, ka yi gwamna kuma ka sauke nauyin da ka ke kanka. Ba bukatar zubar ma ka da mutunci, domin zubar ma ka mutunci tamkar zubar da mutuncin dukkan ajin ‘yan siyasa ne” Inji Atiku Abubakar.

A nan Atiku wanda jigo ne a sabuwar jam’iyyar hadaka ta ADC da Elrufai ke ciki, ya yi gargadin irin wannan yunkuri da ya zayyana da take hakkin Dan’adam ke iya haddasa juyin juya hali.

Kamar sun hada baki da Elrufai kan batun jiran Elrufa’in ya dawo gida gabanin daukar wani mataki ta hanyar mika ma sa takardar gayyata a hukumance maimakon yunkurin cafke shi kenan ta wannan hanyar aiki da cikawa.

Jama’a dai tun farko sun yi dafifi su ka hana jami’an Efcc yunkurin kama Elrufai cewa hakan ba zai yiwu ba sai an bi ta hanyar da su ke ganin ta dace.

Tsohon gwamnan ya yi wata magana da wasu ke ganin ta wuce yanayin wani dan kasa gama-gari ya iya fada ya kwana lafiya yayin da ya shaidawa jami’an Efcc ko shugaban kasa ba zai fada ma sa abun da zai yi ba “ko shugaban kasa ba zai fada mi ni abunda zan yi ba

Hukumomi dai sun amshe fasfo din Elrufai kuma da alamu zai amsa gayyatar Efcc a tsanake.

Hukuamr ta yaki da cin hanci ta sha nanata ba ta daukar mataki kan wani haka kawai sai ta samu hujjoji kwarara.

Kakakin hukumar Dele Oyewole na cewa Efcc na hukunta mutane kan laifinsu ba don wata wariya ko tsana ba.

In za a tuna shi ma tsohon ministan shari’a Abubakar Malami ya samu kansa a wannan dambarwa bayan samun beli daga kotu amma jami’an DSS su ka sake awun gaba da shi.

Ga Rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya Daga Abuja

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/AUD-20260213-WA0000.mp3
Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu
Next Post: Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba Labarai
Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai
  • Kasar Amurka Tabada Tabbacin Bawa Ukraine Tsaron Shekarun 15 Amurka
  • Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
  • Ukraine Ta Mika Wa Amurka Daftarin Yarjejeniya Da Rasha Sauran Duniya
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.