Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro
Published: February 20, 2026 at 12:19 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da takwaran aikinsa na Jamus Chancellor Friedrich Merz, sun tattauna ta wayar tarho kan batun tsaro, makamashi lantarki, da kuma kayayyakin more rayuwa, kamar yadda ofishin shugaban kasan ya fada a ranar Alhamis.

A maganar da suka yi ranar Laraba, na tsawon minti tara, shugabannin biyu sunyi magana kan sake farfado da aikin samar da wutan lanatarki a Najeriya da ya tsaya, da babban kamfanin kasar Jamus SIEMENS zai yi, haka kuma Najeriya zata sayi jirage masu saukar ungulu wadanda ba sababbi bane daga Jamus.

Shugaba Tinubu ya gayawa Mr. Mertz cewa Najeriya tana bukatar taimako wajen sabunta hanyoyin samarda wutan lantarki a kasar.

Wata yarjejeniyar da Najeriya ta kulla da kamfanin SIEMENS a shekara ta 2019, kamfanin zai sabunta hanyoyin raba wutan lantarki da bankunan Jamus za su dauki nauyin aikin, da zimmar idan aka kamala aikin zai samar da wutan lantarki MegaWatts dubu 7, zuwa 2021, sannan ya karu zuwa megawatt dubu 11 zuwa karshen Shekara ta 2023, sai dai aikin ya fuskanci kalubale daban daban da suka hada da kudi, sharuddan gwamnati da makamantar su.

Shugaba Merz na Jamus ya fadawa shugaba Tinubu cewa kamfanin SIEMENS zai yi aikin, kuma a shirye Bankin Deutsche yake ya samar da kudaden tafiyar da aikin, kamar yadda sanarwa daga ofishin shugaban kasar ya fada.

Najeriya da Jamus suna da huldar difilomasiyya na tsawon shekaru 65.

Labarai, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato
Next Post: Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi

Karin Labarai Masu Alaka

Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026 Wasanni
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.