Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato
Published: February 19, 2026 at 3:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 19, 2026

Rundunar ‘yan sandan jihar Filato tace ta tura jami’anta dake bangaren tantance bam, zuwa wurin hakar ma’adinai na kwal, a Kampanin Zurak dake karamar hukumar Wase, inda a kalla mutane talatin da bakwai suka rasa rayukansu, wassu ishirin da shida aka kai su asibiti, sanadiyyar shakar gubar gas a lokacin da suke aiki.

A wata sanarwa da ta aike wa manema labarai, rundunar ‘yan sandan a Jihar Filato tace binciken da ta fara gudanarwa ya nuna cewa guba dake cikin Ma’adanai lead oxide da sulfur da carbon monoxide ne suka hallaka masu hakar ma’adinan.

Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan a jihar Filato, Alfred Alabo ya sanya wa hannu ta nuna da cewa babu alamar tashin bam a wurin, duk da haka dai jami’an sun sauki samfurin dutse da rairayi da ma’adinan dake wurin don ci gaba da bincike.

Shugaban matasan Wase, Shafi’u Sambo yace ya zuwa yanzu mutane talatin da takwas ne suka rasa ransu a wurin hakar ma’adinan na Kamfanin Zurak.

A halin da ake ciki kuma, gwamnatin jihar Filato ta jajanta wa iyalan wadanda suka rasun da kuma addu’ar sauki wa wadanda ke jinya a asibiti.

A sanarwa da komishinan yada labarai da sadarwa na jihar Filato, Madam Joyce Ramnap ta sanya wa hannu, gwamnatin tace zata karfafa dokar harkokin hakar ma’adinai don tsaron lafiyar al’umma.

Sanarwar tace gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya sha alwashin hadin gwiwa da hukumomin tarayya da sauran hukumomin dake kula da ayyukan hakar ma’adinai, kamfanoni da al’umman yankin da ake hakar ma’adinan don aiwatar da matakan kariya.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/GUBAR-GAS-YA-HALLAKA-MASU-HAKAR-MAADINAI-A-FILATO.mp3
Bidiyo, Labarai

Post navigation

Previous Post: Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Man Fetur A Najeriya Afrika
Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba Labarai
Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
  • Amurkawa Sun Nuna Bacin Rai Saboda Yawaita Kashe ‘Yan Kasar Amurka
  • Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
  • Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta Afrika
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC Siyasa
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • Najeriya Da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.