Rundunar ‘yan sandan jihar Filato tace ta tura jami’anta dake bangaren tantance bam, zuwa wurin hakar ma’adinai na kwal, a Kampanin Zurak dake karamar hukumar Wase, inda a kalla mutane talatin da bakwai suka rasa rayukansu, wassu ishirin da shida aka kai su asibiti, sanadiyyar shakar gubar gas a lokacin da suke aiki.

A wata sanarwa da ta aike wa manema labarai, rundunar ‘yan sandan a Jihar Filato tace binciken da ta fara gudanarwa ya nuna cewa guba dake cikin Ma’adanai lead oxide da sulfur da carbon monoxide ne suka hallaka masu hakar ma’adinan.
Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan a jihar Filato, Alfred Alabo ya sanya wa hannu ta nuna da cewa babu alamar tashin bam a wurin, duk da haka dai jami’an sun sauki samfurin dutse da rairayi da ma’adinan dake wurin don ci gaba da bincike.
Shugaban matasan Wase, Shafi’u Sambo yace ya zuwa yanzu mutane talatin da takwas ne suka rasa ransu a wurin hakar ma’adinan na Kamfanin Zurak.
A halin da ake ciki kuma, gwamnatin jihar Filato ta jajanta wa iyalan wadanda suka rasun da kuma addu’ar sauki wa wadanda ke jinya a asibiti.
A sanarwa da komishinan yada labarai da sadarwa na jihar Filato, Madam Joyce Ramnap ta sanya wa hannu, gwamnatin tace zata karfafa dokar harkokin hakar ma’adinai don tsaron lafiyar al’umma.

Sanarwar tace gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya sha alwashin hadin gwiwa da hukumomin tarayya da sauran hukumomin dake kula da ayyukan hakar ma’adinai, kamfanoni da al’umman yankin da ake hakar ma’adinan don aiwatar da matakan kariya.
Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos


