Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo
Published: February 19, 2026 at 2:48 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mutum biyu sun mutu a wani rikici yayin zaɓen shugabannin APC a Ondo

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Ondo ta tabbatar da mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu uku sakamakon rikicin da ya ɓarke a taron zaɓen shugabannin mazabu na jam’iyyar APC a Idanre.

Mai magana da yawun rundunar, Abayomi Jimoh, ya ce lamarin ya faru ne a ranar 18 ga Faburairu da misalin ƙarfe 11:05 na safe bayan samun kiran gaggawa daga DPO na yankin.

Ya bayyana cewa Kwamishinan ‘yan sanda, Adebowale Lawal, ya tura rundunonin musamman tare da haɗin gwiwar jami’an Civil Defense domin daƙile rikicin da dawo da zaman lafiya.

Rahotanni sun nuna cewa an kai hari ga mutane biyar tare da banka wa mota wuta, inda uku daga cikin waɗanda aka kai wa harin na karɓar magani, yayin da aka tabbatar da mutuwar biyu a asibiti.

‘Yan sanda sunce ana ci gaba da bincike domin gano waɗanda suka aikata laifin, tare da ɗaukar matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a jihar.

Najeriya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi
Next Post: Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC Afrika
Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Kasar Jamus Ta Haramtawa Yara Kasa Da Shekaru 14 Hawa Dandalin Sada Zumunta Labarai
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami Afrika
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kama Maharan Bom Din Maiduguri Tsaro
  • Akwai Yiwuwar Farashin Mai Zai Kara Tashi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.