Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa
Published: April 19, 2026 at 1:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Raya Kogin Benue ta sanar da wani shiri na musamman domin inganta ayyukan noma ga manoma a yankin Dam ɗin Daɗinkowa da ke jihar Gombe a Najeriya

Manajan Daraktan Hukumar, Dr. Mahmud Sanusi Muhammad, ne ya bayyana wannan shiri ne a yayin ƙaddamar da rabon takin zamani mai rangwame, wanda aka tsara domin ƙara yawan amfanin gona a jihar Gombe.

Domin rage barazanar namun daji, musamman giwayen ruwa Dr. Muhammad ya ce hukumar na duba yiwuwar samar musu da abinci a wurare masu nisa da gonakin mutane. Ya ce wannan zai taimaka wajen jawo su daga yankunan noma, tare da kare rayuwar manoma da amfanin gonakinsu.

Bugu da ƙari, Manajan Daraktan ya bayyana cewa ana ci gaba da aikin gyaran hanyoyin ruwa (canals), domin kai ruwa zuwa gonaki masu nisa, wanda hakan zai taimaka wajen bunƙasa noman ban-ruwa a duk tsawon shekara.

Sabon Manajan Yanki, Abubakar Muhammad Bello Sarkin Shanu, ya jaddada cewa shirin takin zamani mai rangwame wanda haɗin gwiwa ne tsakanin hukumar da kamfanoni masu zaman kansu na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da wadatar abinci a ƙasa.

Ya ce: “A tsarin da ake ciki yanzu, manoma za su biya rabin kuɗin taki kafin karɓa, sannan su biya ragowar bayan girbi ko dai da kuɗi ko da amfanin gona.”

Sarkin Shanu ya ƙara da cewa irin wannan haɗin gwiwa na da muhimmanci, yana mai jaddada cewa dole ne jama’a su daina dogaro da gwamnati kaɗai.

“Dole mu koya yin haɗin gwiwa domin gina abubuwa masu amfani. Idan aka yi la’akari da yadda yawan jama’a da buƙatu ke ƙaruwa, gwamnati kaɗai ba za ta iya biyan dukkan buƙatunmu ba,” in ji shi.

Wakilan kamfanonin haɗin gwiwa, Yero Farms da Wababe Integrated Agric Ventures, wanda Alhaji Nasiru Umar ya wakilta, sun yaba da ƙoƙarin UBRBDA wajen tallafawa manoma. Sun kuma roƙi waɗanda suka amfana da shirin da su kiyaye amana ta hanyar biyan bashin da aka ba su a kan lokaci.

Taron ya kuma samu saƙonnin fatan alheri daga shugabannin al’umma daban-daban, ciki har da Comrade Musa Umar na Dandalin Matasan Hina da kuma Alhaji Sadik Shehu, Shugaban Ƙungiyar Masu Amfani da Ruwa (WUA).

Duk da yabon shirin, sun roƙi a ƙara faɗaɗa hanyoyin ban-ruwa tare da inganta abubuwan more rayuwa, musamman samar da ruwan sha mai tsafta da wutar lantarki mai ɗorewa a yankin Daɗinkowa da maƙwabtanta.

Da take jawabi a madadin waɗanda suka amfana, Mrs. Doris Yakubu, shugabar mata ta WUA, ta bayyana muhimmancin haɗa mata cikin harkokin noma a yankin.

Ta ce mata a Daɗinkowa na taka rawa sosai a fannin noma, kuma ta nuna kwarin gwiwa cewa tallafin takin zamani zai ƙara yawan amfanin gonakinsu.

Ta kuma tabbatar da cewa manoma za su cika alkawarin biyan bashin da aka ba su bayan samun girbi mai kyau.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma
Next Post: Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya
Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
Hanyar Gombe Dukku Darazo Ta Zamo Abun Damuwa Ga Al’ummar Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
  • Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • Kasar Jamus Ta Haramtawa Yara Kasa Da Shekaru 14 Hawa Dandalin Sada Zumunta Labarai
  • Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
  • Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.