Wata babbar kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta yanke hukunci cewa tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, ya cancanci kuma zai iya tsayawa takarar Shugaban Ƙasa a zaɓen shekarar 2027.
Kotun, wadda ke ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Peter Lifu na Babbae Kotun Tarayya da ke Abuja, ta bayyana hukuncin ne a ranar Talata, inda ta tabbatar da cewa babu wani tanadi na doka da ya hana Jonathan sake tsayawa takara.
Wannan hukunci ya biyo bayan shari’ar da wani mai shigar da ƙara, Johnmary Jideobi, ya shigar, yana neman kotu ta hana Jonathan tsayawa takara ko kuma bayyana kansa a matsayin ɗan takara a kowane jam’iyya a zaɓen 2027.
A cikin ƙarar, mai shigar da ƙara ya kuma nemi kotu ta hana Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, Independent National Electoral Commission, karɓa, sarrafawa ko bayyana sunan Jonathan a matsayin ɗan takara.
Sai dai mai shari’a Peter Lifu ya yi watsi da waɗannan buƙatu, inda ya bayyana cewa Jonathan na da cikakken haƙƙi a ƙarƙashin kundin tsarin mulki na 1999 da aka gyara, domin shiga takarar shugaban ƙasa.
Hukuncin kotun ya kuma zo ne a daidai lokacin da wani ɓangare na jam’iyyar PDP, ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki, ya bayar da rangwame (waiver) ga Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.
Jonathan, wanda ya mulki Najeriya daga shekarar 2010 zuwa 2015, ya sha kaye a zaɓen 2015 a hannun Muhammadu Buhari, lamarin da ya zama tarihi a siyasar ƙasar saboda shi ne shugaban ƙasa na farko da ya amince da shan kaye a zaɓen sake tsayawa mulki.
Hukuncin kotun na zuwa ne a matsayin wani muhimmin sauyi da ka iya ƙara ƙaimi a tseren siyasar 2027 da ake tunkara.


