Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara
Published: May 26, 2026 at 11:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata babbar kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta yanke hukunci cewa tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, ya cancanci kuma zai iya tsayawa takarar Shugaban Ƙasa a zaɓen shekarar 2027.

Kotun, wadda ke ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Peter Lifu na Babbae Kotun Tarayya da ke Abuja, ta bayyana hukuncin ne a ranar Talata, inda ta tabbatar da cewa babu wani tanadi na doka da ya hana Jonathan sake tsayawa takara.

Wannan hukunci ya biyo bayan shari’ar da wani mai shigar da ƙara, Johnmary Jideobi, ya shigar, yana neman kotu ta hana Jonathan tsayawa takara ko kuma bayyana kansa a matsayin ɗan takara a kowane jam’iyya a zaɓen 2027.

A cikin ƙarar, mai shigar da ƙara ya kuma nemi kotu ta hana Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, Independent National Electoral Commission, karɓa, sarrafawa ko bayyana sunan Jonathan a matsayin ɗan takara.

Sai dai mai shari’a Peter Lifu ya yi watsi da waɗannan buƙatu, inda ya bayyana cewa Jonathan na da cikakken haƙƙi a ƙarƙashin kundin tsarin mulki na 1999 da aka gyara, domin shiga takarar shugaban ƙasa.

Hukuncin kotun ya kuma zo ne a daidai lokacin da wani ɓangare na jam’iyyar PDP, ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki, ya bayar da rangwame (waiver) ga Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.

Jonathan, wanda ya mulki Najeriya daga shekarar 2010 zuwa 2015, ya sha kaye a zaɓen 2015 a hannun Muhammadu Buhari, lamarin da ya zama tarihi a siyasar ƙasar saboda shi ne shugaban ƙasa na farko da ya amince da shan kaye a zaɓen sake tsayawa mulki.

Hukuncin kotun na zuwa ne a matsayin wani muhimmin sauyi da ka iya ƙara ƙaimi a tseren siyasar 2027 da ake tunkara.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
Next Post: Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP

Karin Labarai Masu Alaka

An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Game Da Matsalar Tsaro A Najeriya Najeriya
Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Man Fetur A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
  • Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
  • Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika
  • Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Kiwon Lafiya
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.