Sanata Muhammadu Danjuma Goje yayi watsi da samakon zaben dake yawo inda yace bashida tushe, mara inganci ne.
Tsohon Gwamnan jihar Gombe kuma Sanata Mai ci Karo na hudu Danjuma Goje yace sakamakon zaben dake yawo bashida tushe balle madafa.
Goje dai shine Sanata mai wakiltar mazabar Gombe ta tsakiya a majalisar dattawan Najeriya, Wanda yake kan kujerar tun 2011.
A yayin da yake jawabi a madadin Sanatan Goje hadimin sa Alhaji Ahmed Isa Kashere, yace sakamakon zaben fidda gwani na yankin Akko da Yamaltu Deba da akayi a ranar Litinin basu kammala ba kuma ba’a sanar ba!
A yayin da ya zargi wasu gidajen jaridu da sabbin kafafen sada zumunta da yada labarin karya mara inganci.
Sanata Danjuma Goje yayi kira ga magoya bayan sa da yan jam’iyar da al’ummar mazabar sa dasu kwantar da hankalin su kuma suyi watsi da sakamakon zaben dake yawo bashida tushe kuma mara inganci.
Ya kara da cewa “A madadin Sanata Danjuma Goje ina shawartan al’ummar mazabar Gombe ta tsakiya wanda suka hada da kananan hukumomin Akko da Yamaltu Deba suyi watsi da wannan labarin kanzon kurege dake yawo daga makiya jam’iyar muta APC me daraja.
Bari mu kawar muku da shakku, muna masu tabbatar muku cewa har yanzu sakamakon zaben fidda gwani ba’a baiyana ba tukun na, saboda kamar yadda uwar jam’iya ta kasa ta tsara sakamakon zaben za’a fade sane a ofishin jam’iyar APC na Kasa dake Abuja.
Ya sake kira da masoya da magoya baya da al’umma baki daya da su kara hakuri sujira sanarwan sakamakon zaben a hukumance.
A matsayin sa na dattijo kuma mai gabatar da doka da oda, mai fada aji a jihar Gombe ya tsaya ne akan ra’ayin sa na bin ka’idodi da tsari sannan da kiyaye dokokin da jam’iyar APC ta gindiya


