Kasar Rwanda ta ce zata janye dakarun ta daga yankin Cabo Delgado na kasar Mozambique, inda suke taimakawa wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda, idan kokarin nata baya samun goyon baya na tallafin kudade daga kasashen waje.

Dakarun da aka aike su tun shekarar 2021 bayan da Mozambique ta bukaci hakan, sun taimaka wajen kawo kwanciyar hankali a yankunan da da ke fama da ‘yan ta’adda, a cewar mai magana da yawun gwamnatin Rwanda a Yolande Makolo, a shafin sa na sada zumunta na X.
A wani rahoto na mujallar kasuwanci da kasafin kudi ta Bloomberg, tallafin da Tarayyar Turai ke bawa dakarun zai kare a watan Mayu, kuma babu wani shiri na sabunta shi.
Jami’an Tarayyar Turai a Brussels basu ce komai game da tambayoyin da aka yi musu kan sha’anin ba.
Da yake nuni kan rahoton na Bloomberg, Yolande Makolo yace, dorewar dakarun ya ta’allaka ne ga samun isassun kudade, wanda ake gani. Ya kara da cewa, idan ba’a ganin amfanin aikin dakarun na Rwanda da ake kira RDF a Cabo Delgado, suna da dama su bukaci gwamnati ta kawo karshen yarjejeniyar yaki da ta’addanci, su fice daga wajen.


