Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda
Published: December 5, 2025 at 1:36 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta kama wani likita da ake zargi da jigilar kayan magani daga Jihar Sokoto zuwa wasu kungiyoyin masu garkuwa da mutane da ke aiki a sassan jihar Kwara.

An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin Facebook na gidan Gwamnatin Jihar Kwara a ranar Juma’a.

Rahotanni sun ce an kama likitan ne a Jebba, cikin Karamar Hukumar Moro, bayan samun bayanan sirri da suka hada shi da wata hanyar kai magunguna ga kungiyoyin ‘yan bindigar.

An ce kama ire iren sa, yana daya daga cikin matakan da ake dauka domin dakile hanyoyin da ke tallafa wa miyagun kungiyoyi a yankin.

Majiyoyin tsaro sun ce ‘yan bindigar sun kara yawan neman kulawar likita, musamman wajen magance raunukan harbin bindiga da suke samu yayin artabu da jami’an tsaro.

Wannan karuwar bukatar magunguna ta jawo hankalin hukumomin tsaro da ke sa ido kan zirga-zirgar haramtattun kayayyaki.

Wani jami’in tsaro ya yi gargadin cewa cibiyoyin lafiya da ke kusa da dazuka na iya fuskantar karin barazana, domin miyagun mutane na iya kai farmaki don neman kulawar gaggawa.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC
Next Post: Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025,

Karin Labarai Masu Alaka

Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki Labarai
UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura Afrika
Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi Tsaro
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka
Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
  • Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
  • Afirka Ta Kudu Zata Fuskanci Koma Baya A Bangaren Samar Da Ayyukanyi Afrika
  • UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.