Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kama Maharan Bom Din Maiduguri
Published: January 7, 2026 at 5:48 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sojoji sun kama ƙarin mutane 8 da ake zargi da hannu a harin bam na masallacin Borno

Sojojin rundunar Operation Hadin Kai sun kama ƙarin mutane takwas da ake zargi da hannun su a harin bam da wani mai tayar da kai ya kai a wani masallaci da ke Maiduguri, jihar Borno.

Wannan na zuwa ne kasa da kwana uku bayan sojoji sun kama wanda ake zargin shine ya shirya harin, mai suna Sheriff Umar, a babban birnin jihar.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa harin kunar bakin wake ya faru ne a ranar 24 ga Disamba na shekarar 2025, lokacin da wani mai tayar da bam ya tarwatsa na’urar fashewa (IED) a cikin wani masallaci da ke kasuwar Gamboru a Maiduguri, wanda ya yi sanadin mutuwar akalla masu ibada biyar tare da jikkata wasu 35.

A cikin wata sanarwa, jami’in hulda da jama’a na rundunar Operation hadin kai, Sani Uba, ya bayyana cewa an kama waɗannan mutanen ne a wani samame da aka gudanar a unguwar Yan Lemu da ke karamar hukumar Mubi ta Kudu a Jihar Adamawa.

Ya ce, Binciken da aka yi a gidan da ake zargin ya haifar da gano maƙudan kuɗaɗe, wayoyin hannu, takardun shaidar tantancewa, katunan ATM, kayan ado da wasu kayan sirri na amfanin kai, waɗanda a halin yanzu haka ake gudanar binciken shaidu akan su.

Ya ƙara da cewa, wani da ake tsare da shi tuni ya tantance wasu daga cikin manyan masu hannu a lamarin a matsayin waɗanda suka kawo kayan da aka yi amfani da su wajen ƙera bam ɗin.

Ya ƙara da cewa, Sauran mutanen da ke zaune a gidan suma an samo alaƙarsu da wannan ƙungiya.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda
Next Post: Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa

Karin Labarai Masu Alaka

An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
Dakarun Pakistan Da Afghanistan Sunyi Arrangama Labarai
Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar Tsaro
Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
  • Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.