Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

An Kama Maharan Bom Din Maiduguri
Published: January 7, 2026 at 5:48 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sojoji sun kama ƙarin mutane 8 da ake zargi da hannu a harin bam na masallacin Borno

Sojojin rundunar Operation Hadin Kai sun kama ƙarin mutane takwas da ake zargi da hannun su a harin bam da wani mai tayar da kai ya kai a wani masallaci da ke Maiduguri, jihar Borno.

Wannan na zuwa ne kasa da kwana uku bayan sojoji sun kama wanda ake zargin shine ya shirya harin, mai suna Sheriff Umar, a babban birnin jihar.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa harin kunar bakin wake ya faru ne a ranar 24 ga Disamba na shekarar 2025, lokacin da wani mai tayar da bam ya tarwatsa na’urar fashewa (IED) a cikin wani masallaci da ke kasuwar Gamboru a Maiduguri, wanda ya yi sanadin mutuwar akalla masu ibada biyar tare da jikkata wasu 35.

A cikin wata sanarwa, jami’in hulda da jama’a na rundunar Operation hadin kai, Sani Uba, ya bayyana cewa an kama waɗannan mutanen ne a wani samame da aka gudanar a unguwar Yan Lemu da ke karamar hukumar Mubi ta Kudu a Jihar Adamawa.

Ya ce, Binciken da aka yi a gidan da ake zargin ya haifar da gano maƙudan kuɗaɗe, wayoyin hannu, takardun shaidar tantancewa, katunan ATM, kayan ado da wasu kayan sirri na amfanin kai, waɗanda a halin yanzu haka ake gudanar binciken shaidu akan su.

Ya ƙara da cewa, wani da ake tsare da shi tuni ya tantance wasu daga cikin manyan masu hannu a lamarin a matsayin waɗanda suka kawo kayan da aka yi amfani da su wajen ƙera bam ɗin.

Ya ƙara da cewa, Sauran mutanen da ke zaune a gidan suma an samo alaƙarsu da wannan ƙungiya.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda
Next Post: Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa

Karin Labarai Masu Alaka

Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Karu A Karshen 2024 Rediyo
  • Kungiyoyi Sunyi Hasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.