Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade
Published: December 21, 2025 at 8:15 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 21, 2025

Tuhume-tuhumen cin zarafi yasa Molde FK ta dakatar da Daniel dan Najeriya.

Dan wasan tsakiya na kwallon kafa ta Najeriya mai tashe Daniel Daga, yana fuskantar shari’a bayan ana tuhume shi da laifin cin zarafin wa ta mata ba tare da izini ba a kasar Norway.

Kungiyarsa ta Molde FK, ta tabbatar da wannan lamari, wanda ya haifar da cece kuce a tsakanin ‘yan wasan Eliteserien da kuma ‘yan wasan kwallon kafa ta Najeriya, a wata sanarwa da ta aka fitar a ranar Juma’a.

Matashin dan wasan mai shekaru 18, wanda kwanan nan ya koma buga kwallon kafa a Turai, an dakatar da shi daga dukkan ayyukan kungiyar, da suka hada da notsa jiki da wasannin gasa, yayin da ake ci gaba da shari’ar.

A cewar mai gabatar da kara, tuhume-tuhumen sun samo asali ne daga wani lamari da ya faru a lokacin kakar wasa ta farko a Norway.

Duk da cewar ba’a sanar da cikakken bayanin abun da ya faru ba, don kare bangarorin da abin ya shafa, Kotun Gundumar Nordmøre da Romsdal ta tsara zaman sauraren karar a watan Maris na 2026.

An ruwaito cewa dan wasan ya kasance mai bada hadin kai a duk lokacin binciken farko, yana halartar da amsa duk tambayoyin da ‘yan sanda suka yi masa.

Duk da cewa ya dawo Najeriya tun daga lokacin, ana sa ran zai koma Norway don fuskantar shari’ar a bazara mai zuwa.

Molde FK, ɗaya daga cikin fitattun ƙungiyoyi ne a Norway, ta ɗauki mataki mai ƙarfi kan wannan lamarin.

Shugaban ƙungiyar Odd Ivar Moen ya jaddada muhimmancin tuhumar yayin da ya amince da wahalar da lamarin ke haifarwa ga duk masu ruwa da tsaki a ƙungiyar.

“Wannan lamari ne mai mahimmanci, kuma muna ɗaukar tuhumar da muhimmanci,” in ji Moen.

“Irin waɗannan shari’o’in suna da matuƙar wahala ga duk wanda abin ya shafa.

Abin da ya fi muhimmanci shi ne mu yi aiki da gaskiya da kuma tabbatar da adalci da girmama dukkan ɓangarorin.

Ƙungiyar ta kuma ɗauki matakin tuntuɓar lauyoyin mai ƙara, tana mai amincewa da “nauyin na sirri” da shari’ar ta ɗora wa wanda abin ya shafa.

Duk da tuhumar da ake yi masa a hukumance, wadda ya ke wakiltar Daniel Daga a shara’ance ya tabbatar da cewa ba shi da laifi.

Lauyansa, Astrid Bolstad, ya tabbatar da cewa yayin faruwar lamarin jima’in ɗan wasan tsakiya ya tabbatar da cewa anyi shi bisa amince duk kanin su gaba ɗaya. Babu wata shaida ko zargin tashin hankali ko barazana da aka samu a lokacin

Daniel Daga ya je ƙungiyar ta Molde kafin kakar wasa ta 2025 a matsayin ɗaya daga cikin ‘yan wasan tsakiya masu tasowa a Afirka.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote
Next Post: An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja 

Karin Labarai Masu Alaka

AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025. Wasanni
‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
Sabon Jadawalin Gasar Kwalon Kafa Ta Turai 2026 Wasanni
Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
  • Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.