Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa
Published: July 21, 2026 at 12:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Dokokin jihar Filato ta yi karin haske kan kudirin dokar da ke neman samar da tsarin alawus na wata-wata ga tsofaffin ‘yan majalisar jihar, bayan ce-ce-ku-cen da kudirin ya haifar a tsakanin al’umma.

A makon da ya gabata ne majalisar ta gabatar da kudirin dokar, wanda ya tsallake karatu na farko da na biyu a rana guda. Kudirin na neman bai wa tsofaffin shugabannin majalisa da mambobin da suka kammala wa’adinsu damar samun alawus na wata-wata mai kama da pansho.

Shugaban Kwamitin Kudi na Majalisar Dokokin Jihar Filato, kuma mamba mai wakiltar Rukuba/Irigwe, Eli Bako Ankala, wanda ya gabatar da kudirin, ya ce manufarsa ita ce ‘yan majalisar da ke kan mulki su ware wani kaso daga alawus dinsu domin tallafa wa tsofaffin ‘yan majalisar.

Ya bayyana cewa kudaden ba za su fito daga gwamnatin zartarwa ba, sai dai daga gudunmawar da ‘yan majalisar za su rika bayarwa daga alawus dinsu.

Sai dai kungiyoyin farar hula da na kwadago a jihar sun yi watsi da kudirin, suna zargin cewa ba a bayyana cikakkun bayanansa ga jama’a ba.

Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) reshen Jihar Filato, Kwamared Eugene Manji, ya ce sun bai wa majalisar wa’adin zuwa ranar 30 ga watan Yuli ta janye kudirin, yana mai gargadin cewa idan ba a yi hakan ba, za su dauki matakin kulle harabar majalisar.

A halin yanzu dai ana ci gaba da sa ido kan yadda rikicin ra’ayi tsakanin majalisar da kungiyoyin farar hula da na kwadago zai kaya idan wa’adin ya cika.

Daga Jos, Zainab Babaji ta aiko mana da rahoto

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/07/AUD-20260721-WA0024.mp3
Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS
Next Post: Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere Afrika
Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Aikin Kwamitin Sayar Da Kaddarorin Gwamnati Afrika
  • Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • Magoya Bayan Obi Sun Yi Tutsu Gabanin Zaben 2027 Siyasa
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.